Home Taska Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa

Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa

Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa

 

Mutum shida sun rasu, yayin da wasu huɗu suka jikkata bayan tsawa ta faɗa kansu a ƙauyen Dadiri-Tirgali da ke gundumar Garum a Ƙaramar Hukumar Ganye ta Jihar Adamawa.

Lamarin ya faru ne ranar Lahadi yayin da mamatan da waɗanda suka jikkata ke girbin gyaɗa ruwan sama kamar da bakin ƙwarya yana kwarara.

Shaidu sun ce huɗun da suka tsira suna karɓar magani a Babban Asibitin Ganye, yayin da al’ummar yankin suka shiga jimami sakamakon ibtila’in.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Ganye, Daniel Kamsobbi, da ya tabbatar da faruwar lamarin ya jajanta wa iyalan mamatan.

Ya ƙara da cewa an sallami wata uwa da ɗanta daga asibiti bayan an tabbatar da ƙoshin lafiyarsu, yayin da mutum biyu ke ci gaba da karɓar magani.

Ya ce an umarci ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro su binciki musabbabin lamarin domin taimakawa wajen wayar da kan al’umma, musamman manoma da ke yawan aiki a gonaki lokacin damina.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp