Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar Adamawa
Mutum shida sun rasu, yayin da wasu huɗu suka jikkata bayan tsawa ta faɗa kansu a ƙauyen Dadiri-Tirgali da ke gundumar Garum a Ƙaramar Hukumar Ganye ta Jihar Adamawa.
Lamarin ya faru ne ranar Lahadi yayin da mamatan da waɗanda suka jikkata ke girbin gyaɗa ruwan sama kamar da bakin ƙwarya yana kwarara.
Read Also:
Shaidu sun ce huɗun da suka tsira suna karɓar magani a Babban Asibitin Ganye, yayin da al’ummar yankin suka shiga jimami sakamakon ibtila’in.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Ganye, Daniel Kamsobbi, da ya tabbatar da faruwar lamarin ya jajanta wa iyalan mamatan.
Ya ƙara da cewa an sallami wata uwa da ɗanta daga asibiti bayan an tabbatar da ƙoshin lafiyarsu, yayin da mutum biyu ke ci gaba da karɓar magani.
Ya ce an umarci ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro su binciki musabbabin lamarin domin taimakawa wajen wayar da kan al’umma, musamman manoma da ke yawan aiki a gonaki lokacin damina.










