Home Taska NMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba 

NMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba 

NMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man Kan Sayar da Farashin Fetur

 

Hukumar Kula da Harkokin ta Najeriya (NMDPRA) ta yi gargaɗin cewa za ta hukunta gidajen man da ke sayar da man fetur a farashin da bai yi daidai da farashin ɗanyen mai a kasuwar duniya ba.

A cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, George Ene-Ita, ya fitar a ranar Laraba, ya ce hukumar na sane da raguwar farashin ɗanyen mai a duniya, inda ya ce dole ne farashin man fetur ya zo daidai da yadda farashin yake, kamar yadda dokar albarkatun mai ta 2021 a ƙasar ta tanada.

Ya ce hukumar ta riga ta gargaɗi kamfanonin kasuwancin mai da su guji ƙara farashi domin cin ribar da ta wuce ƙa’ida.

NMDPRA ta ce ana sa ido kan gidajen mai, kuma za a ɗauki matakin a kan duk wanda aka samu da laifi.

Wannan gargaɗi na zuwa ne bayan kiran da ƙaramin ministan albarkatun man fetur, Sanata Heineken Lokpobiri, ya yi ga hukumomin da su ɗauki mataki kan dillalan man.

Ya ce bayan dakatar da yaƙi tsakanin Iran da Amurka, ƴan Najeriya na sa ran ganin an rage farashin man fetur a ƙasar.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp