Home General Hedkwatar tsaron Najeriya ta magantu kan ceto Janar Tsiga

Hedkwatar tsaron Najeriya ta magantu kan ceto Janar Tsiga

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce babu kuɗin fansa da aka biya kafin sakin tsohon shugaban Hukumar yi wa Ƙasa Hidima a Najeriya NYSC, Manjo Janar Mahrazu Tsiga, mai ritaya daga hannun ƴanbindiga.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hedkwatar tsaron Birgediya-Janar Tukur Gusau ya fitar, ya ce sojoji sun yi amfani da dabarun karfi da kuma bayanan sirri wajen ceto Janar Tsiga.

“Tun bayan sace Janar Tsiga ranar 7 ga watan Fabrairu, sojoji ba su yi ƙasa a gwiwa ba. Sun kai samame ta sama da kuma ƙasa a ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Faskari da kuma Kankara inda ake kyautata zaton masu garkuwan sun ajiye shi,” a cewar Tukur Gusau.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sun yi ta aiki tukuru babu dare ba rana wajen nema da kuma ceto tsohon shugaban na NYSC.

An dai yi garkuwa da shi ne ranar 5 ga watan Fabrairu, a garin mahaifarsa ta Tsiga da ke karamar hukumar Bakori na jihar Katsina – tare da wasu mutum 13.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp