Home General Hedkwatar tsaron Najeriya ta magantu kan ceto Janar Tsiga

Hedkwatar tsaron Najeriya ta magantu kan ceto Janar Tsiga

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce babu kuɗin fansa da aka biya kafin sakin tsohon shugaban Hukumar yi wa Ƙasa Hidima a Najeriya NYSC, Manjo Janar Mahrazu Tsiga, mai ritaya daga hannun ƴanbindiga.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hedkwatar tsaron Birgediya-Janar Tukur Gusau ya fitar, ya ce sojoji sun yi amfani da dabarun karfi da kuma bayanan sirri wajen ceto Janar Tsiga.

“Tun bayan sace Janar Tsiga ranar 7 ga watan Fabrairu, sojoji ba su yi ƙasa a gwiwa ba. Sun kai samame ta sama da kuma ƙasa a ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Faskari da kuma Kankara inda ake kyautata zaton masu garkuwan sun ajiye shi,” a cewar Tukur Gusau.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sun yi ta aiki tukuru babu dare ba rana wajen nema da kuma ceto tsohon shugaban na NYSC.

An dai yi garkuwa da shi ne ranar 5 ga watan Fabrairu, a garin mahaifarsa ta Tsiga da ke karamar hukumar Bakori na jihar Katsina – tare da wasu mutum 13.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp