Home General Gwamnati ta gaza kare al’ummar jihar Zamfara – Amnesty

Gwamnati ta gaza kare al’ummar jihar Zamfara – Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International a Najeriya ta ce gwamnatin ƙasar ta gaza wajen kare lafiya da dukiyoyin jama’a, la’akari da yadda ƴan bindiga ke kashe mutane a jihar Zamfara ba tare da ƙauƙautawa ba.

Daraktan Ƙungiyar Malam Isa Sanusi wanda ke tsokaci akan kazamin harin da ƴan bindiga suka kai yankin Ɗangulbi dake ƙaramar hukumar Maru a Jihar Zamfara, suka kuma hallaka mutane 26, yace gwamnatin ba wai ta gaza ne saboda rashin jami’an tsaro ko kuma kudin da za’ayi aikin tabbatar da tsaro ba, sai dai saboda san rai da nuna rashin kula da rayuwar jama’a da kuma mayar da hankali akan siyasa.

Sanusi ya ce Najeriya na da isassun kuɗin da za’a sayawa sojoji duk abinda suke buƙata domin murkushe waɗannna yan bindiga da suka hana jama’a zaman lafiya a jihohin Zamfara da Kebbi da Sokoto da Neja da kuma Kaduna, amma saboda rashin mayar da hankali akan lamarin, ga shi an ɗauki dogon lokaci ana kashe mutane ba tare da magance matsalar ba.

Daraktan ya ce abinda ya faru a ranar alhamis ya daɗa jefa tsoro da kuma fargaba a tsakanin mutanen Ɗangulbi, inda ya bayyana shi a matsayin abin takaici da ya afka akan jama’a.

Sanusi ya ce waɗannan ƴan bindiga sun dade suna ɗora haraji akan manoma da yan kasuwa a garuruwa, yayin da waɗanda suka ki biya kuma su gamu da fushin su ta hanyar kisa da kuma azabtarwa.

Daraktan ya ce mutanen wannan yanki na cikin yanayin bala’i, ta inda zuwa wasu wurare ma baya yiwuwa, sai mako mako idan sojoji sun raka matafiya, kafin su samu maslaha.

Satar dukiya da fyade ga mata da ‘ƴan mata ya zama ruwan dare, in ji shi, yayin da gwamnati ta kasa ɗaukar matakan da suka dace domin sauke nauyin da ya rataya akan ta, abinda ya sa wasu daga cikin waɗannan mutane ke cewa ba su san amfanin gwamnati a gare su ba.

A karshe, Sanusi ya ce gwamnati ta gaza domin ba zata iya kare lafiyar jama’a ba, inda ya ƙara da cewa a shekarar 2018 ya ziyarci waɗannan yankuna kuma ya ga abinda ke faruwa, kuma har ya zuwa yau babu wani abinda ya sauya daga irin ukubar da suke sha daga hannun irin waɗannan mutane.

Daraktan ya ce duk da ikrarin ɗaukar sabbin matakai na gwamnati, ya tabbata cewar waɗannan mataki basa aiki, saboda haka ya zama wajibi a zauna a tsakanin hukumomi da mutane domin nazari akan abinda ya dace, koda kuwa ɗauko sojojin haya ne ko taimako daga ƙasashen ƙetare.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp