Home Taska Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

Rundunar Soji

Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta’adda

 

Dakarun Rundunar sojoji na Operation FANSAN YAMMA sun bankaɗo wata masana’antar ƙera bindigogi haramtacciya da ake zargin tana samar da makamai ga ’yan ta’adda a Jihar Kebbi.

Mai magana da yawun rundunar, Laftanar Kanar Aliyu Danja ya ce dakarun sun kai samamen ne bayan samun sahihan bayanan sirri kan wani wuri da ake amfani da shi wajen ƙera da rarraba bindigogi.

A yayin binciken da aka gudanar, an ƙwato bindigogin AK-47 guda biyar da aka ƙera a cikin gida, sannan an kama mutum biyu da ake zargin masu ƙera da safarar makaman ne.

Ya ce, an gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran hukumomin tsaro, yana mai cewa hakan wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin da ake yi na daƙile yaɗuwar makamai ba bisa ƙa’ida ba da kuma dakile hanyoyin da ’yan ta’adda ke samun kayan aiki.

A cewarsa, waɗanda aka kama na tsare a hannun sojoji domin ci gaba da bincike, yayin da ake farautar sauran mambobin ƙungiyar da masu ɗaukar nauyinsu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp