Home Taska Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan...

Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan Matasa

Gwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba – Ministan Matasa

 

Ministan Raya Matasa na Najeriya, Ayodele Olawande, ya bayyana cewa har yanzu gwamnatin tarayya ba ta amince da sauya kayan masu yi wa ƙasa hidima na NYSC zuwa kayan Kampala ba.

A wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X, ministan ya ce rahotannin da ke cewa an amince da amfani da Kampala a maimakon kaki sun fassara kalamansa ba daidai ba, bayan wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels.

Ya ce lokacin hirar ya ambaci Adire da Ankara ne kawai a matsayin wasu daga cikin shawarwarin da ake tattaunawa a kan su, yana mai jaddada cewa har yanzu ba a yanke hukunci kan irin kayan ko tsarin da za a yi amfani da shi ba.

Ya ce, “Manufata ita ce in bayar da misalai na wasu daga cikin shawarwarin da aka gabatar yayin tattaunawa. Ban sanar da cewa an amince da wani irin kaya ya maye gurbin kakin NYSC na yanzu ba.”

Ministan ya ce duk wata matsaya da za a cimma za ta kasance ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki tare da la’akari da abin da ya fi amfani ga shirin NYSC da kuma Najeriya baki ɗaya.

Mista Olawande ya ce “sauye-sauyen da ake shiryawa na da nufin inganta shirin ta hanyar ƙara wa matasa damar samun aikin yi, bunƙasa harkokin kasuwanci, ƙarfafa haɗin kan ƙasa, inganta ayyukan yi da kuma sauƙaƙa musu shiga rayuwar aiki bayan kammala karatu.”

Ya kuma ce “bai kamata muhawarar da ake yi kan kayan NYSC ta mamaye hankalin jama’a fiye da manyan sauye-sauyen da gwamnati ke shiryawa domin ƙarfafa matasan Najeriya da kuma bunƙasa ci gaban ƙasar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp