Home SIYASA Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci...

Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci ba – Atiku

Bai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na’abba da Zargin Cin Hanci ba – Atiku

 

Tsohon Mataimakin Shugaban Najeriya, Atiku Abubakar ya yi watsi da sabon zargin da tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo ya yi masa, yana mai cewa ƙoƙari ne na ɓata masa suna domin ba wa ɗan takarar da yake goyon baya gabanin zaɓen 2027.

A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu ya fitar Atiku ya ce bai dace Obasanjo ya danganta marigayi tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Umar Na’Abba da zargin cin hanci ba, alhali ba ya raye don ya kare kansa.

Ya kuma ce, idan har akwai hujjar aikata laifin kamar yadda aka yi zargin ya kamata gwamnatin Obasanjo ta ɗauki mataki tun lokacin da lamarin ya faru.

Atiku ya yi zargin cewa, lokacin da aka sake tayar da batun na da alaƙa da shirye-shiryen siyasar zaben 2027, yana mai cewa tsohon shugaban ƙasar ya kamata ya fito fili ya bayyana ɗan takarar da yake goyon baya maimakon amfani da tsofaffin zarge-zarge wajen janyo ra’ayin jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
China ba za ta Bayar ko ta Sayar wa Iran Makamai ba a Kowane h Hali - TrumpBai Dace Obasanjo ya Danganta Marigayi Ghali Na'abba da Zargin Cin Hanci ba - AtikuGarkuwa da Mutane: Dakarun Sojin Najeriya Sun Kama Mutane 5 a Jihar Yobe Sojojin Najeriya na Neman ɗaya Daga Cikin Jami'inta Ruwa a Jallo, Kan Zargin Sayar wa Ƴan bindiga Kakin SojiYaɗa Farfaganda da ƙiyayya Kan Gwamnati ba Zai Kawo ƙarshenta ba - MatawalleMawallafin PRNigeria Ya Fitar Da Littafin Tarihin Rayuwarsa Akan Rigimar NIPSS Yayin Da IMPR Ta Bayyana Cigaba Mai Karfi A Tsakiyar ShekaraShugaban Amurka ya Yaba wa Shugaba Tinubu Kan Matakan da Yake ɗauka Wajen Yaƙi da Ta'addanciBinciken Gaskiya: Shin Gajimaren ne ya ɓulɓulowa ƙasa a Hanyar Abuja Zuwa Kaduna?HRW ta Zargin Hukumomin Najeriya da Rashin Adalci ga Ƴan  ƙungiyar Boko HaramHukuncin da Kotu ta Yanke wa Matashin da ya  Yunƙurin Satar Motar Yan SandaMutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗe
X whatsapp