Mutane 5 Sun Mutu Bayan Kwale-Kwale ya Kife a Jihar Neja
Mutum biyar ne suka mutu bayan da wani kwale-kwale ya kife a Kogin Kudi da ke ƙauyen Shaba Woshi a ƙaramar hukumar Katcha ta jihar Neja, a cewar rundunar ’yan sandan jihar.
Read Also:
A cikin wata sanarwa, rundunar ta ce jami’anta sun garzaya zuwa wurin da hatsarin ya faru bayan samun rahoton lamarin.
Ta ƙara da cewa hatsarin ya yi sanadin mutuwar mutum biyar, kuma an samu nasarar gano gawarwakin dukkansu daga kogin.
Rundunar ta bayyana cewa an yi jana’izar mamatan.
Sashen Binciken Manyan Laifuka (SCID) da ke Minna na ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin hatsarin.











