Home Taska Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu...

Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun 

Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun 

Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC) ta zargi Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da hana dubban mata Musulmi masu sanya hijabi kaɗa ƙuri’arsu a zaɓen gwamnan jihar Osun da aka gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026.

A cikin wata sanarwa da daraktan ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar, MURIC ta yi ikirarin cewa lamarin ya faru a wurare da dama na jihar, inda ta ce an hana wasu mata masu hijabi yin zaɓe sai bayan sun cire hijabinsu.

Kungiyar ta bayyana hakan a matsayin tauye haƙƙin zaɓe da kuma cin mutuncin mata Musulmi.

MURIC ta ɗora alhakin lamarin kan shugabancin INEC, tana mai cewa hukumar ta gaza wayar da kan jami’anta na dindindin da na wucin gadi game da ’yancin addini.

Kungiyar ta kuma ce tana da bidiyon wata mata mai hijabi da ta yi korafin cewa an hana ta yin zaɓe saboda suturar da take sanyawa.

Kungiyar ta sake kira da a cire shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, tare da zargin cewa abin da ta kira tsoratar da mata Musulmi masu hijabi ya yi tasiri a sakamakon zaɓen.

Haka kuma MURIC ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta binciki zarge-zargen, tana mai gargadin cewa irin wannan matsala na iya sake faruwa a babban zaɓen shekarar 2027 idan ba a ɗauki mataki ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Anambara: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'addan IPOB/ESN, Sun Kwato MakamaiHukumar Kwastam ta Kano ta Mika Magungunan da ba a yi wa Rijista ba ga NAFDAC, ta Kuma yi Alƙawarin Tsaurara Matakan Aiki.Operation HADIN KAI: Harin Jiragen Sama Ya Kawar da 'Yan Ta'adda 36 a BornoFamadewa, Ribadu da Shirin Tsaron Kwanaki 90: Yadda YAShuaib ya Binciki Sanarwar OnanugaLabarin NIPSS Ya Bayyana Cin Zarafin Babban Jami'in Sojan Ruwa, Rear Admiral AA MustaphaƊaliban PRNigeria Sun Yaba da Gyare-Gyaren FRSC, Sun Nemi Ƙarin Ƙarfafa Sadarwa Kan Tsaron HanyaYadda Dalibai 4 Almajirai Suka Mutu Bayan Cin Kife da Ake Zargi da Guba a KanoSojoji Sun Ceto Mutane 14 da Aka Sace a Dajin KatsinaTinubu Ya Nada Abel Enitan A Matsayin Sabon Shugaban Ma'aikatan TarayyaRundunar Sojin Ruwan Najeriya ta Ceto Mutane 22 Daga Hannun Ƴan Fashin Teku Kimanin Malamai 200 ne Suka bar Jami'ar KASU - ASUUHukumar EFCC ta Gurfanar da Mutumin da ake Zargi da Damfarar Maniyyata Aikin HajjiKashi 40 Cikin 100 Kawai na Cibiyoyin Kiwon Lafiya a Duniya ke da Tsabta - MDDDakarun Sojin Najeriya Sun Daƙile Yunƙurin Garkuwa da Mutane a Zamfara
X whatsapp