Ƙungiyar MURIC ta Zargi INEC da Hana Mata Masu Hijabi Kaɗa ƙuri’arsu a Zaɓen Jihar Osun
Ƙungiyar Kare Haƙƙin Musulmi (MURIC) ta zargi Hukumar Zaɓe mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da hana dubban mata Musulmi masu sanya hijabi kaɗa ƙuri’arsu a zaɓen gwamnan jihar Osun da aka gudanar ranar 15 ga Agusta, 2026.
A cikin wata sanarwa da daraktan ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola, ya fitar, MURIC ta yi ikirarin cewa lamarin ya faru a wurare da dama na jihar, inda ta ce an hana wasu mata masu hijabi yin zaɓe sai bayan sun cire hijabinsu.
Kungiyar ta bayyana hakan a matsayin tauye haƙƙin zaɓe da kuma cin mutuncin mata Musulmi.
MURIC ta ɗora alhakin lamarin kan shugabancin INEC, tana mai cewa hukumar ta gaza wayar da kan jami’anta na dindindin da na wucin gadi game da ’yancin addini.
Kungiyar ta kuma ce tana da bidiyon wata mata mai hijabi da ta yi korafin cewa an hana ta yin zaɓe saboda suturar da take sanyawa.
Kungiyar ta sake kira da a cire shugaban INEC, Farfesa Joash Amupitan, tare da zargin cewa abin da ta kira tsoratar da mata Musulmi masu hijabi ya yi tasiri a sakamakon zaɓen.
Haka kuma MURIC ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta binciki zarge-zargen, tana mai gargadin cewa irin wannan matsala na iya sake faruwa a babban zaɓen shekarar 2027 idan ba a ɗauki mataki ba.











