Home General ‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa...

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina

‘Yan sanda sun sami nasarar halaka ‘yan ta’addan da ake nema ruwa a jallo a jihar katsina,
Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da kakakin rundunar SP GAMBO ISAH, ANIPR ya fita a madadin kwamishinan ‘yan sanda jihar, sanarwa tace ‘yan ta’addan sun hadar da Na-Iraqi, Na-Masari.
Sanarwa mai dauke da kwanan watan 13 ga watan Disambar 2022 tace da misalin karfe 7:30 jami’an ‘yansan sun sami kiran cewa ‘yan bindiga sun tasamma yankin Sokoto – Rima Quarters dake karamar hukumar Dutsinma a jihar Katsina suna harbi kan mai uwa da wabi da bindiga kirar AK47, da nufin yin garkuwa da wani mazaunin yankin.
Babu bata lokaci dakarun dake lura da yankin suka garzaya wurin domin kai dauki, da isar su suka fara musayar wuta da ‘yan bindigar suka kuma sami nasarar hallaka 2 daga cikin su wadanda kuma suna jadawalin wadanda ake nema ruwa a jallo da suka hadar da Abu Na-Iraqi da Abu Na-Masari suka kuma sami nasarar kwato bindiga kirar AK47.
Jami’an ‘Yan sanda sun shiga bincike domin gano wadan suka tsere da raunukan harbi a jikin su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp