Home General Gwamnatin Nijeriya ta kawo karshen Gwajin Corona ga matafiya

Gwamnatin Nijeriya ta kawo karshen Gwajin Corona ga matafiya

Mahukunta a Najeriya sun ce daga yanzu matafiya sun dai na nuna sakamakon basa dauke da cutar korona idan sun isa ko kuma za su yi tafiya zuwa wata kasa.

Hukumar kula da zirga zirgar jiragen sama ta kasar ta ce an dauki matakin hakan ne bayan tabbatar da cewa a yanzu ba kasafai ake samun wadanda suka kamu da cutar ba a kasar dama sauran kasashen duniya.

Hukumar ta ce daga yanzu duk wani matafiyi daga gida Najeriya da ma wadanda suka dawo daga wata kasar ba za a bukaci sakamakon gwajin cutar da ya nuna basa dauke da ita ba.

A baya dai wajibi ne ga duk matafiya suyi gwajin cutar kafin tafiya, haka ma wadanda suka dawo dole su nuna sakamakon gwajin da ya nuna basa dauke da ita.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp