Home General Mayakan ISWAP sun Hallaka DPO a Jihar Borno

Mayakan ISWAP sun Hallaka DPO a Jihar Borno

Rahotannin daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa wasu da ake zargin mayakan kungiyar boko haram tsagin ISWAP sun hallaka baturen dan sanda Sunday Pius a karamar hukumar Marte dake jihar.

Haka kuma harin ‘yan ta’addan yayi sanadiyyar raunata wasu jami’an ‘yan sanda guda biyu.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da faruwa lamarin ta bakin Kakakin ta ASP Kenneth Daso ya a birnin Maiduguri a yammacin ranar talata.

ASP Kenneth yace sun sami kiran gaggawa cewa ‘yan ta’addan sun hallaka baturen ‘yan sanda dake lura da yankin New Marte a ranar Litinin wannan ne ya sanya kwamishinan ‘yan sandna jihar ya bada umarni yin bincike.

An ruwaito cewa mayakan sun shiga cikin garin ne da misalign karfe 7 da mintuna 30 na daren ranar litinin, in da suka kai hari kan jami’an lafiya, sai dai an ruwaito jami’an lafiyar sun tsallake rijiya da baya.

Bayan da jami’an lafayar sukayi gudun tsira zuwa ofishin ‘yan sandan ne ‘yan ta’addan suka afkawa ofishin nan suka hallaka baturen ‘yan sandan tare da raunata jami’an ‘yan sanda guda biyu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp