Home General Mayakan ISWAP sun Hallaka DPO a Jihar Borno

Mayakan ISWAP sun Hallaka DPO a Jihar Borno

Rahotannin daga jihar Borno dake Arewa maso gabashin Nijeriya na bayyana cewa wasu da ake zargin mayakan kungiyar boko haram tsagin ISWAP sun hallaka baturen dan sanda Sunday Pius a karamar hukumar Marte dake jihar.

Haka kuma harin ‘yan ta’addan yayi sanadiyyar raunata wasu jami’an ‘yan sanda guda biyu.
Rundunar ‘yan sandan jihar ta tabbatar da faruwa lamarin ta bakin Kakakin ta ASP Kenneth Daso ya a birnin Maiduguri a yammacin ranar talata.

ASP Kenneth yace sun sami kiran gaggawa cewa ‘yan ta’addan sun hallaka baturen ‘yan sanda dake lura da yankin New Marte a ranar Litinin wannan ne ya sanya kwamishinan ‘yan sandna jihar ya bada umarni yin bincike.

An ruwaito cewa mayakan sun shiga cikin garin ne da misalign karfe 7 da mintuna 30 na daren ranar litinin, in da suka kai hari kan jami’an lafiya, sai dai an ruwaito jami’an lafiyar sun tsallake rijiya da baya.

Bayan da jami’an lafayar sukayi gudun tsira zuwa ofishin ‘yan sandan ne ‘yan ta’addan suka afkawa ofishin nan suka hallaka baturen ‘yan sandan tare da raunata jami’an ‘yan sanda guda biyu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp