Home General NAHCON ta kwashe Alhazai sama da Dubu 10 zuwa Saudiya

NAHCON ta kwashe Alhazai sama da Dubu 10 zuwa Saudiya

Hukumar Alhazai ta kasar nan ta ce kawo yanzu ta kwashe maniyyatan aikin hajjin bana 10,675 daga kasar zuwa kasa mai tsarki.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan harkokin yada labarai ta hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar, inda tace sun sami nasarar jigilar Maniyyata 4,665 ta jirgin FlyNas, sai jirgin Max Air da ya kwashe maniyyatan 4,479 jirgin Air Peace ya yi jigilar 1,531.

Ta kara da cewa kawo yanzu dai hukumar bata sami rahoton wani jirgi da aka soke tashin sa sai dai jirgin maniyatan jihar kwara da aka daga tashin sa a daren talata.

Haka kuma jihar Nassarawa ta zama jiha ta farko data fara kamala jigilar maniyyatan ta kimanin 1,794 na shekarar 2024 haka kuma jihar Oyo da rundunar sojoji ake sa ran zasu kamala jigilar zuwa dare.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp