Home General NAHCON ta kwashe Alhazai sama da Dubu 10 zuwa Saudiya

NAHCON ta kwashe Alhazai sama da Dubu 10 zuwa Saudiya

Hukumar Alhazai ta kasar nan ta ce kawo yanzu ta kwashe maniyyatan aikin hajjin bana 10,675 daga kasar zuwa kasa mai tsarki.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mataimakin daraktan harkokin yada labarai ta hukumar Fatima Sanda Usara ta fitar, inda tace sun sami nasarar jigilar Maniyyata 4,665 ta jirgin FlyNas, sai jirgin Max Air da ya kwashe maniyyatan 4,479 jirgin Air Peace ya yi jigilar 1,531.

Ta kara da cewa kawo yanzu dai hukumar bata sami rahoton wani jirgi da aka soke tashin sa sai dai jirgin maniyatan jihar kwara da aka daga tashin sa a daren talata.

Haka kuma jihar Nassarawa ta zama jiha ta farko data fara kamala jigilar maniyyatan ta kimanin 1,794 na shekarar 2024 haka kuma jihar Oyo da rundunar sojoji ake sa ran zasu kamala jigilar zuwa dare.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp