Home General Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

Jagoran jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya nuna matuƙar damuwa kan yadda matsalar tsaro ke ta ’kara munana a Najeriya, yana mai gargaɗin cewa matsalolin tsaro da ke faruwa yanzu na neman ya fi ƙarfin gwamnati.

Ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X.

Kwankwaso, wanda ya taɓa zama gwamnan Kano, ya ce alamu na nuna cewa matsalolin tsaro da ke faruwa yanzu ka iya zama babbar barazana ga haɗin kai da kwanciyar hankalin ƙasa.

A cikin saƙonsa, ya ce: “Dukkan alamu na nuna cewa rashin tsaro na neman ya fi ƙarfin gwamnatin. Wannan na bayyana a yadda take barin jihohi su kafa ƙungiyoyin tsaro na ƴan sa kai ba tare da horo na musamman ba.”

“Wannan mataki, ko da an yi shi da kyakkyawar niyya, ya haddasa yaɗuwar ƙananan makamai da manyan makamai a faɗin ƙasa.” in ji shi.

Kwankwaso ya kuma nuna damuwa kan yadda ake samun ƙaruwa a tsangwama da azabtar da ’yan Najeriya musamman daga wasu yankuna.

Ya ce “wasu ’yan siyasa ma sun fara amfani inda ya ƙara da cewa kalaman ƙiyayya a kafofin sada zumunta na ƙara rura wutar rikici da raba kan al’umma.

Kwankwaso ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta hanzarta ɗaukar mataki kafin lamura su lalace gaba ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp