Home General Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa...

Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafi

Gwamnatin Jihar Kano ta fara aikin tantancewa tare da ɗaukar bayanan ’yan kasuwar da gobarar kasuwar Singer ta shafa domin tsara yadda za a bi matakan ba su tallafi.

Rahotanni sun nuna cewa gobarar ta tashi ne da yammacin ranar Asabar inda ta ƙone shaguna da tebura fiye da 1,500, lamarin da ya jawo asarar dukiya mai yawa ga ’yan kasuwa.

Tuni gwamnatin tarayya ta bai wa waɗanda abin ya shafa tallafin Naira biliyan biyar, baya ga gudummawar da wasu hukumomi da daidaikun jama’a suka bayar.

Hukumomin jihar sun sanar da fara aikin tantance ’yan kasuwar ta hannun Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jiha wato SEMA.

Hukumar ta bayyana cewa duk lokacin da aka samu iftila’i irin wannan, sukan je su ƙididdige tare da ɗaukar bayanan waɗanda abin ya shafa domin sanin yadda za a taimaka musu.

Shugaban hukumar, Isyaku Abdullahi Kubarachi, ya ce suna gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA reshen jihar Kano.

SEMA ta ce aikin zai ɗauki kwanaki biyar ana yi, bayan haka za su rubuta rahoto su miƙa wa gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf, wanda ake sa ran zai yi nazari tare da kafa kwamitin da zai kula da raba tallafin ga waɗanda suka cancanta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp