Home Labarai Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa

Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, kuma jigo a jam’iyyar haɗaka ta ADC ya nuna damuwa kan ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka samu a zaɓen ƙananan hukumomin Abuja na ranar Asabar, yana mai zargin cewa hakan na nuna yadda ake yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya wallafa a shafinsa na X, ya bayyana cewa yawan jama’ar da suka fito zaɓen Abuja bai kai kashi 20 cikin 100 ba wata alama da ke nuna halin da dimokuraɗiyyar Najeriya ke ciki a yanzu.

Ya ce “Ƙarancin masu kaɗa kuri’a da aka samu a babban birnin ƙasar ba abin mamaki ba ne, illa sakamakon yanayin siyasa da ya ce ya cika da rashin haƙuri da tsoratarwa da kuma rage ƙarfin muryoyin adawa.”

A cewarsa, “idan ’yan ƙasa suka daina yarda cewa ƙuri’unsu na da tasiri, dimokuraɗiyya ya fara mutuwa.”

Ya ƙara da cewa “abin da ake gani ba sakamakon rashin sha’awar zaɓe kaɗai ba ne, illa sakamakon shugabanci da ke takura tsarin dimokuraɗiyya.”

Ya ce “dimokuraɗiyya ba za ta cika ba idan babu ƙarfi a ɓangaren adawa, babu gasa ta gaskiya a siyasa, kuma babu amincewar jama’a.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp