Home Labarai Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa

Atiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, kuma jigo a jam’iyyar haɗaka ta ADC ya nuna damuwa kan ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka samu a zaɓen ƙananan hukumomin Abuja na ranar Asabar, yana mai zargin cewa hakan na nuna yadda ake yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasa a ƙarƙashin shugabancin Bola Tinubu.

A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya wallafa a shafinsa na X, ya bayyana cewa yawan jama’ar da suka fito zaɓen Abuja bai kai kashi 20 cikin 100 ba wata alama da ke nuna halin da dimokuraɗiyyar Najeriya ke ciki a yanzu.

Ya ce “Ƙarancin masu kaɗa kuri’a da aka samu a babban birnin ƙasar ba abin mamaki ba ne, illa sakamakon yanayin siyasa da ya ce ya cika da rashin haƙuri da tsoratarwa da kuma rage ƙarfin muryoyin adawa.”

A cewarsa, “idan ’yan ƙasa suka daina yarda cewa ƙuri’unsu na da tasiri, dimokuraɗiyya ya fara mutuwa.”

Ya ƙara da cewa “abin da ake gani ba sakamakon rashin sha’awar zaɓe kaɗai ba ne, illa sakamakon shugabanci da ke takura tsarin dimokuraɗiyya.”

Ya ce “dimokuraɗiyya ba za ta cika ba idan babu ƙarfi a ɓangaren adawa, babu gasa ta gaskiya a siyasa, kuma babu amincewar jama’a.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp