Home Labarai Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

Jamhuriyar Nijar ta amince da kundin ayyukan Ƙungiyar Kasashen Sahel (AES) na shekara ta biyu wadda ta haɗa da Mali da Burkina Faso, kafin taron ministoci da za a gudanar a Ouagadougou daga 24 zuwa 26 ga watan Fabrairu, kamar yadda jaridar gwamnati ta ANP ta ruwaito a ranar 21 ga Fabrairu.

Firaminista Ali Mahamane Lamine Zeine ya gana da ministoci da mambobin kwamitin ƙasa na AES a ranar 21 ga Fabrairu domin daidaita matsayi kafin taron yankin.

Mataimakiyar Shugabar kwamitin, Bayard Mariama Gamatie, ta ce Burkina Faso ta raba wani kundin aiki, wanda Nijar ta gyara bisa ginshiƙai uku da suka haɗa da tsaro da diflomasiyya, ci gaban ƙasa, da tsaro da kare iyaka.

“An amince da kundin gaba ɗaya, dangane da shawarwarin gyare-gyaren Nijar,” in ji Gamatie.

Rahoton ya nuna cewa ministocin Nijar sun duba kundin sun kuma yi gyare-gyare da sake fasalta wasu abubuwa, sannan sun bayar da shawarwari don taron ƙwararru da zai biyo baya.

An kafa AES a shekarar 2023, bayan da ƙasashen uku suka janye daga Ƙungiyar ECOWAS, domin tsara manufofi na tsaro da diflomasiyya, da ci gaban ƙasa tsakanin ƙasashen Sahel.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp