Home Labarai Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

Nijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyu

Jamhuriyar Nijar ta amince da kundin ayyukan Ƙungiyar Kasashen Sahel (AES) na shekara ta biyu wadda ta haɗa da Mali da Burkina Faso, kafin taron ministoci da za a gudanar a Ouagadougou daga 24 zuwa 26 ga watan Fabrairu, kamar yadda jaridar gwamnati ta ANP ta ruwaito a ranar 21 ga Fabrairu.

Firaminista Ali Mahamane Lamine Zeine ya gana da ministoci da mambobin kwamitin ƙasa na AES a ranar 21 ga Fabrairu domin daidaita matsayi kafin taron yankin.

Mataimakiyar Shugabar kwamitin, Bayard Mariama Gamatie, ta ce Burkina Faso ta raba wani kundin aiki, wanda Nijar ta gyara bisa ginshiƙai uku da suka haɗa da tsaro da diflomasiyya, ci gaban ƙasa, da tsaro da kare iyaka.

“An amince da kundin gaba ɗaya, dangane da shawarwarin gyare-gyaren Nijar,” in ji Gamatie.

Rahoton ya nuna cewa ministocin Nijar sun duba kundin sun kuma yi gyare-gyare da sake fasalta wasu abubuwa, sannan sun bayar da shawarwari don taron ƙwararru da zai biyo baya.

An kafa AES a shekarar 2023, bayan da ƙasashen uku suka janye daga Ƙungiyar ECOWAS, domin tsara manufofi na tsaro da diflomasiyya, da ci gaban ƙasa tsakanin ƙasashen Sahel.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp