Home General Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar, ya ce har yanzu sojojin Najeriya 11 na maƙale a ƙasar Burkina Faso bayan saukar gaggawa da wani jirgi da suke ciki ya yi a ƙasar.

Rahoton ya ce lamarin ya faru ne tun ranar 8 ga Disamba, lokacin da jirgin ya yi saukar gaggawa a ƙasar inda ƙungiyar ƙasashen Sahel (AES) ta zargi jirgin sojin Najeriya da keta sararin samaniyar Burkina Faso ba tare da izini ba.

A cewar rahoton, shugaban gwamnatin soji ta Mali, Assimi Goïta, ya bayyana saukar jirgin a matsayin matakin da ya saɓa wa ƙa’idojin ƙasashen duniya

Rundunar Sojin Saman Najeriya kuwa ta ce jirgin yana kan hanyarsa ce ta zuwa ƙasar Portugal lokacin da ya samu tangarɗar na’urar da ta tilasta masa yin saukar gaggawa a ƙasar.

Kungiyar AES – ta ƙunshi ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar wadanda suka fice daga ƙungiyar ECOWAS a watan Janairu, bayan takunkuman da aka sanya musu sakamakon juyin mulki a ƙasashensu.

Sun sanar da ficewarsu daga ƙungiyar ne a daidai lokacin da Najeriya ke jagorantar ECOWAS.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp