Home Labarai Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari

Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari

Wata babbar kotun tarayya mai zamanta a garin Gwarimpa da ke babban birnin tarayya Abuja ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige a gidan yarin Kuje.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC ce ta gurfanar da tsohon ministan a gaban mai shari’a Mariam Hassan bisa tuhume-tuhume guda takwas da suka danganci cin hanci da rashawa.

Ngige, wanda ya kasance minista a zamanin mulkin tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya isa harabar kotun ne da misalin ƙarfe 8:10 na safiyar yau Juma’a tare da rakiyar jami’an EFCC.

Hukumar ta zargi Ngige da aikata laifukan ne a lokacin da yake minista, musamman a lokacin da yake kula da hukumar bayar da tallafi ta Najeriya wato NSITF.

A tuhuma ta farko, ana zargin cewa daga Satumban 2015 zuwa Mayun 2023, Ngige ya yi amfani da matsayinsa a lokacin matsayin tsohon minista wajen bai wa abokansa cin gajiyar kwangila ba bisa ka’ida.

Sai dai a zaman kotun, tsohon ministan ya musanta laifukan da ake tuhumarsa da su.

Mai shari’a Mariam ta ɗage shari’ar zuwa Litinin domin sauraron buƙatar neman belinsa, sannan ta bayar da umarni a tsare shi a gidan yarin Kuje har zuwa ranar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp