Home Labarai Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari

Kotu ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige gidan yari

Wata babbar kotun tarayya mai zamanta a garin Gwarimpa da ke babban birnin tarayya Abuja ta tura tsohon ministan ƙwadago Chris Ngige a gidan yarin Kuje.

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC ce ta gurfanar da tsohon ministan a gaban mai shari’a Mariam Hassan bisa tuhume-tuhume guda takwas da suka danganci cin hanci da rashawa.

Ngige, wanda ya kasance minista a zamanin mulkin tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya isa harabar kotun ne da misalin ƙarfe 8:10 na safiyar yau Juma’a tare da rakiyar jami’an EFCC.

Hukumar ta zargi Ngige da aikata laifukan ne a lokacin da yake minista, musamman a lokacin da yake kula da hukumar bayar da tallafi ta Najeriya wato NSITF.

A tuhuma ta farko, ana zargin cewa daga Satumban 2015 zuwa Mayun 2023, Ngige ya yi amfani da matsayinsa a lokacin matsayin tsohon minista wajen bai wa abokansa cin gajiyar kwangila ba bisa ka’ida.

Sai dai a zaman kotun, tsohon ministan ya musanta laifukan da ake tuhumarsa da su.

Mai shari’a Mariam ta ɗage shari’ar zuwa Litinin domin sauraron buƙatar neman belinsa, sannan ta bayar da umarni a tsare shi a gidan yarin Kuje har zuwa ranar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Sojoji da PTDF Sun Tattauna Hadin Gwiwa Kan Fasahar Jiragen Sama Marasa Matuki, Kwarewar Dijital da TsaroHukumar FAAC ta Raba Kudin Shiga N2.338trn ga Gwamnatin Tarayya, Jihohi, Kananan Hukumomi a Watan AugustaMinna: 'Mun Sha Fitsarin Mu Don Rayuwa', Wanda ya Tsira ya Bada Labarin Mutuwar Ma'adinai 37 a Cell Din NSCDCNeja ta Sanya Dokar Hana Zirga-zirga na Sa'o'i 24 Bayan Zanga-zangar Kan Mutuwar Ma'aikatan Hako Ma'adinai 37 a Hannun Jami'an NSCDCShugaba Tinubu ya Fusata, ya Umarci Bincike Kan Mutuwar Mahakan Ma'adinai a Hannun NSCDCGwamnatin Tarayya ta Kafa Kwamitin Mutane 10 Domin Binciken Mutuwar Mahakan Ma'adinai 37 a Hannun NSCDC, ta Dakatar da Jami'ai 21Sojoji Sun Ceto Mutane 6, Sun Kwato Shanu 117 Da Motar Camry a Katsina, ZamfaraSojoji Sun Kawar da Harin Ta'addanci a Gajiram, Mairari, Yayin da Kwamandan JAS da Mayaƙi Suka Mika WuyaNasarar Aikin Hajjin 2026 Alama ce ta Shugabancin Tinubu, In Ji Shettima Yayin Karbar Rahoton NAHCON2027: 'Yan Adawa da Suka Rarrabu Ba Za Su Iya Kayar da Tinubu ba – KungiyaSojoji sun kama Mutane Biyu da ake zargin Ƴan kungiyar ISWAP ne a Borno da AdamawaSojoji Sun Ceto Mutane 22 da Aka yi Garkuwa da su, Sun Kwato Babura 3 a Jihar NejaA Legas, Hukumar Kwastam Ta Kwato Naira biliyan 2, Ta Kuma Kama Buhunan Shinkafa 21,000 Cikin Watanni TaraFRSC ta Musanta Zargin Ba da Guraben Daukar Aiki 50 ga Mazabar Ɗan Majalisa na GombeYadda Dalibai da Malamai da Aka Sace a Oyo Suka Tsira Bayan Kwanaki 56 a Hannun Masu Garkuwa – Shaida Ta DSS
X whatsapp