Home Labarai Najeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina...

Najeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina Faso

Mahukunta a Najeriya sun ce jirgin NAF C-130 da ya yi saukar gaggawa a Burkina Faso yayin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa ƙasar Portugal.

Sanarwar da rundunar Sojin saman Najeriya ta fitar ta ce ma’aikatan jirgin sun taso ne daga Legas amma sun lura da wata matsala wanda hakan ya sa aka yi taka-tsan-tsan da sauka a Bobo-Dioulasso na Burkina Faso, filin jirgin sama mafi kusa, lamarin da ya yi daidai ƙa’idojin tsaro da ka’idojin zirga-zirgar jiragen sama na ƙasa da ƙasa.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ma’aikatan rundunar saman Najeriya suna cikin ƙoshin lafiya kuma sun samu kyakkyawar kulawa daga hukumomin da suka karɓi baƙuncinsu, ana ci gaba da shirye-shiryen ci gaba da tafiyar da aikin da suka sanya a gaba.”

Rundunar sojojin saman Najeriya ta yaba da tallafin da aka samu a wannan lokaci tare da tabbatar wa da jama’a cewa za ta ci gaba da jajircewa wajen bin ƙa’idojin aiki da ƙa’idojin tsaro, tare da tabbatar da kare lafiyar ma’aikatanta yayin da take kiyaye dokikoin da kundin tsarin mulki ya tanada.”

Sai dai da alama labarin Najeriya na yadda lamarin ya auku ya ci karo da matsayin gwamnatin mulkin sojan Burkina Faso da kuma ƙungiyar ƙawancen ƙasashen Sahel, waɗanda suka ce jirgin ya shiga sararin samaniyar Burkina Faso ne ba tare da izini ba kuma aka tilasta masa sauka.

Kungiyar ƙasashen Sahel (AES) ta yi alla-wadai da lamarin a matsayin “ketare sararin samaniyarta da kuma keta ƴancin kasashe mambobinta,” tare da bayyana saukar jirgin a matsayin “aikin rashin abokantaka da aka yi ba tare da mutunta dokokin ƙasa da ƙasa da ƙa’idojin sufurin jiragen sama ba.”

Lamarin dai ya zo ne a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar rashin aminta da kuma sauya ƙawance a faɗin yammacin Afirka.

Ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar ne suka kafa Ƙungiyar AES, lamarin da ya sa suka fice daga Ƙungiyar ECOWAS a farkon wannan shekarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp