Home Labarai Najeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina...

Najeriya ta ce jirgin ta ya yi saukar gaggawa ne a Burkina Faso

Mahukunta a Najeriya sun ce jirgin NAF C-130 da ya yi saukar gaggawa a Burkina Faso yayin da ya ke kan hanyarsa ta zuwa ƙasar Portugal.

Sanarwar da rundunar Sojin saman Najeriya ta fitar ta ce ma’aikatan jirgin sun taso ne daga Legas amma sun lura da wata matsala wanda hakan ya sa aka yi taka-tsan-tsan da sauka a Bobo-Dioulasso na Burkina Faso, filin jirgin sama mafi kusa, lamarin da ya yi daidai ƙa’idojin tsaro da ka’idojin zirga-zirgar jiragen sama na ƙasa da ƙasa.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Ma’aikatan rundunar saman Najeriya suna cikin ƙoshin lafiya kuma sun samu kyakkyawar kulawa daga hukumomin da suka karɓi baƙuncinsu, ana ci gaba da shirye-shiryen ci gaba da tafiyar da aikin da suka sanya a gaba.”

Rundunar sojojin saman Najeriya ta yaba da tallafin da aka samu a wannan lokaci tare da tabbatar wa da jama’a cewa za ta ci gaba da jajircewa wajen bin ƙa’idojin aiki da ƙa’idojin tsaro, tare da tabbatar da kare lafiyar ma’aikatanta yayin da take kiyaye dokikoin da kundin tsarin mulki ya tanada.”

Sai dai da alama labarin Najeriya na yadda lamarin ya auku ya ci karo da matsayin gwamnatin mulkin sojan Burkina Faso da kuma ƙungiyar ƙawancen ƙasashen Sahel, waɗanda suka ce jirgin ya shiga sararin samaniyar Burkina Faso ne ba tare da izini ba kuma aka tilasta masa sauka.

Kungiyar ƙasashen Sahel (AES) ta yi alla-wadai da lamarin a matsayin “ketare sararin samaniyarta da kuma keta ƴancin kasashe mambobinta,” tare da bayyana saukar jirgin a matsayin “aikin rashin abokantaka da aka yi ba tare da mutunta dokokin ƙasa da ƙasa da ƙa’idojin sufurin jiragen sama ba.”

Lamarin dai ya zo ne a daidai lokacin da ake samun ƙaruwar rashin aminta da kuma sauya ƙawance a faɗin yammacin Afirka.

Ƙasashen Burkina Faso da Mali da Nijar ne suka kafa Ƙungiyar AES, lamarin da ya sa suka fice daga Ƙungiyar ECOWAS a farkon wannan shekarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp