Home General NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta NDLEA a Najeriya, ta bankaɗo muggan ƙwayoyi da aka ɓoye a wasu manyan ɗakunan ajiyar kayayyaki da kuɗinsu suka tasama sama da naira biliyan shida da miliyan 700 a jihar Lagos.

Wata sanarwa da daraktan sashen yaɗa labarai na hukumar, Femi Babafemi ya fitar tace, yayin samamen da jami’an NDLEA ɗin suka gudanar, sun kuma cafke wani babban dillalin ƙwaya mai suna Onyekachi Pius tare da wasu mutum biyar.

Sanarwar ta ci gaba da cewa, an samu mutanen da aka cafke ɗauke da waɗannan ƙwayoyi a tattare da su, bayan samamen da aka kai maɓoyarsu da ke wani rukunin gidajee da ke Lagos.

Daga cikin kayayyakin da aka gano a hannun su, akwai maganin Tramadol da kuma kodin, wanda ake zargin sun adana ne saboda bikin Kirismeti da ke ƙaratowa.

A cewar NDLEA, manyan motoci aka yi amfani da su wajen fitar da tarin waɗannan muggan ƙwayoyin daga rukunin gidaje na Festac da ke yankin Apple Junction.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp