Home Labarai Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi...

Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi ƙawanya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya umarci hukumomin tsaron ƙasar su tura jami’an da za su zagaye dazukan jihohin Kwara, Kebbi da kuma wasu yankuna na Neja , bayan ƙaruwar ayyukan masu riƙe da makamai a yankunan.

Shugaba Tinubu ya kuma ce, dole ne sojojin sama su kasance suna sanya idanu sosai ba dare ba rana a waɗannan yankuna domin taimakawa sojojin da ke ƙasa aiwatar da ayyukansu cikin sauki.

Umarnin Shugaban ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar taɓarɓarewar rashin tsaro a tsakiyar arewa da Arewa maso Yamma, ciki har da sace masu ibada a Eruku da ke Jihar Kwara, da kuma jerin hare-haren da aka gani a sassan Kebbi da Neja da ta kai ga sace ɗalibai, abin da ya haifar da damuwa a sassan ƙasar da ke yammacin Afirka.

Duk da cewa an samu nasarar ceto mutane da dama, hukumomin tsaro har yanzu na aiki tuƙuru domin ‘yantar da wasu da ake kyautata zaton suna tsare a cikin dazuzzuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp