Home Labarai Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi...

Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi ƙawanya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya umarci hukumomin tsaron ƙasar su tura jami’an da za su zagaye dazukan jihohin Kwara, Kebbi da kuma wasu yankuna na Neja , bayan ƙaruwar ayyukan masu riƙe da makamai a yankunan.

Shugaba Tinubu ya kuma ce, dole ne sojojin sama su kasance suna sanya idanu sosai ba dare ba rana a waɗannan yankuna domin taimakawa sojojin da ke ƙasa aiwatar da ayyukansu cikin sauki.

Umarnin Shugaban ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar taɓarɓarewar rashin tsaro a tsakiyar arewa da Arewa maso Yamma, ciki har da sace masu ibada a Eruku da ke Jihar Kwara, da kuma jerin hare-haren da aka gani a sassan Kebbi da Neja da ta kai ga sace ɗalibai, abin da ya haifar da damuwa a sassan ƙasar da ke yammacin Afirka.

Duk da cewa an samu nasarar ceto mutane da dama, hukumomin tsaro har yanzu na aiki tuƙuru domin ‘yantar da wasu da ake kyautata zaton suna tsare a cikin dazuzzuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp