Home Labarai Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi...

Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi ƙawanya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya umarci hukumomin tsaron ƙasar su tura jami’an da za su zagaye dazukan jihohin Kwara, Kebbi da kuma wasu yankuna na Neja , bayan ƙaruwar ayyukan masu riƙe da makamai a yankunan.

Shugaba Tinubu ya kuma ce, dole ne sojojin sama su kasance suna sanya idanu sosai ba dare ba rana a waɗannan yankuna domin taimakawa sojojin da ke ƙasa aiwatar da ayyukansu cikin sauki.

Umarnin Shugaban ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar taɓarɓarewar rashin tsaro a tsakiyar arewa da Arewa maso Yamma, ciki har da sace masu ibada a Eruku da ke Jihar Kwara, da kuma jerin hare-haren da aka gani a sassan Kebbi da Neja da ta kai ga sace ɗalibai, abin da ya haifar da damuwa a sassan ƙasar da ke yammacin Afirka.

Duk da cewa an samu nasarar ceto mutane da dama, hukumomin tsaro har yanzu na aiki tuƙuru domin ‘yantar da wasu da ake kyautata zaton suna tsare a cikin dazuzzuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp