Home Labarai Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi...

Tinubu ya umarci jami’an tsaro su yi wa dazukan Kwara da Kebbi ƙawanya

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya umarci hukumomin tsaron ƙasar su tura jami’an da za su zagaye dazukan jihohin Kwara, Kebbi da kuma wasu yankuna na Neja , bayan ƙaruwar ayyukan masu riƙe da makamai a yankunan.

Shugaba Tinubu ya kuma ce, dole ne sojojin sama su kasance suna sanya idanu sosai ba dare ba rana a waɗannan yankuna domin taimakawa sojojin da ke ƙasa aiwatar da ayyukansu cikin sauki.

Umarnin Shugaban ya zo ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun karuwar taɓarɓarewar rashin tsaro a tsakiyar arewa da Arewa maso Yamma, ciki har da sace masu ibada a Eruku da ke Jihar Kwara, da kuma jerin hare-haren da aka gani a sassan Kebbi da Neja da ta kai ga sace ɗalibai, abin da ya haifar da damuwa a sassan ƙasar da ke yammacin Afirka.

Duk da cewa an samu nasarar ceto mutane da dama, hukumomin tsaro har yanzu na aiki tuƙuru domin ‘yantar da wasu da ake kyautata zaton suna tsare a cikin dazuzzuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp