Home Labarai Atiku Abubakar ya magantu kan ceto Daliban Kebbi

Atiku Abubakar ya magantu kan ceto Daliban Kebbi

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin Ƙasar kan ceto ɗalibai mata da aka sace a Kebbi da aka yi a baya bayan nan.

Ya ce sako su ba abin da za a gabatar da shi a matsayin nasara ba ne, illa wani abu da ke nuna yadda tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaransa ya wallafa a yau Laraba, ya ce ”lamarin na sake tunatar da al’umma ne cewa ƴan ta’adda na cin karensu babu babbaka a ƙasar, ita kuma gwamnati ta ɓige da sanarwa”.

Jawabin nasa na zuwa ne a matsayin martani game da kalaman mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan yaɗa labarai Bayo Onanuga, a wata hira da ya yi, inda ya ce hukumar tsaro ta DSS da sojoji sun gano inda masu garkuwa da mutanen suke, suka tuntuɓe su kuma aka kai ga nasarar cimma sako yaran ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Ya kuma ce bayan jami’an tsaron sun samu bayanan, ba su kai musu hari ba saboda fargabar kar abin ya rutsa da fararen hular da ke hannunsu.

Sai dai tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi watsi da hujjojin, inda ya ɗiga ayar tambayar kan ‘Me ya sa gwamnati ke tunƙaho da tattaunawa da ƴan ta’adda maimakon hallaka su? Kuma me ya sa ba a kashe kowa ba ko a kama wasu ko kuma a ruguza maboyar su?”

Atiku ya kuma ƙara da cewa bayanan da gwamnatin ta fitar na nuna cewa ƴan ta’adda da ƴan bindiga sun zama kamar wata gwamnati mai zaman kanta da ke yarjejeniya, su karɓi kuɗin fansa, su kuma koma cikin daji daga baya su sake sace wasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp