Home Labarai Atiku Abubakar ya magantu kan ceto Daliban Kebbi

Atiku Abubakar ya magantu kan ceto Daliban Kebbi

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin Ƙasar kan ceto ɗalibai mata da aka sace a Kebbi da aka yi a baya bayan nan.

Ya ce sako su ba abin da za a gabatar da shi a matsayin nasara ba ne, illa wani abu da ke nuna yadda tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaransa ya wallafa a yau Laraba, ya ce ”lamarin na sake tunatar da al’umma ne cewa ƴan ta’adda na cin karensu babu babbaka a ƙasar, ita kuma gwamnati ta ɓige da sanarwa”.

Jawabin nasa na zuwa ne a matsayin martani game da kalaman mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan yaɗa labarai Bayo Onanuga, a wata hira da ya yi, inda ya ce hukumar tsaro ta DSS da sojoji sun gano inda masu garkuwa da mutanen suke, suka tuntuɓe su kuma aka kai ga nasarar cimma sako yaran ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Ya kuma ce bayan jami’an tsaron sun samu bayanan, ba su kai musu hari ba saboda fargabar kar abin ya rutsa da fararen hular da ke hannunsu.

Sai dai tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi watsi da hujjojin, inda ya ɗiga ayar tambayar kan ‘Me ya sa gwamnati ke tunƙaho da tattaunawa da ƴan ta’adda maimakon hallaka su? Kuma me ya sa ba a kashe kowa ba ko a kama wasu ko kuma a ruguza maboyar su?”

Atiku ya kuma ƙara da cewa bayanan da gwamnatin ta fitar na nuna cewa ƴan ta’adda da ƴan bindiga sun zama kamar wata gwamnati mai zaman kanta da ke yarjejeniya, su karɓi kuɗin fansa, su kuma koma cikin daji daga baya su sake sace wasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp