Home Labarai Atiku Abubakar ya magantu kan ceto Daliban Kebbi

Atiku Abubakar ya magantu kan ceto Daliban Kebbi

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya caccaki gwamnatin Ƙasar kan ceto ɗalibai mata da aka sace a Kebbi da aka yi a baya bayan nan.

Ya ce sako su ba abin da za a gabatar da shi a matsayin nasara ba ne, illa wani abu da ke nuna yadda tsaro ke ci gaba da taɓarɓarewa a Najeriya.

A cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labaransa ya wallafa a yau Laraba, ya ce ”lamarin na sake tunatar da al’umma ne cewa ƴan ta’adda na cin karensu babu babbaka a ƙasar, ita kuma gwamnati ta ɓige da sanarwa”.

Jawabin nasa na zuwa ne a matsayin martani game da kalaman mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan yaɗa labarai Bayo Onanuga, a wata hira da ya yi, inda ya ce hukumar tsaro ta DSS da sojoji sun gano inda masu garkuwa da mutanen suke, suka tuntuɓe su kuma aka kai ga nasarar cimma sako yaran ba tare da biyan kuɗin fansa ba.

Ya kuma ce bayan jami’an tsaron sun samu bayanan, ba su kai musu hari ba saboda fargabar kar abin ya rutsa da fararen hular da ke hannunsu.

Sai dai tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya yi watsi da hujjojin, inda ya ɗiga ayar tambayar kan ‘Me ya sa gwamnati ke tunƙaho da tattaunawa da ƴan ta’adda maimakon hallaka su? Kuma me ya sa ba a kashe kowa ba ko a kama wasu ko kuma a ruguza maboyar su?”

Atiku ya kuma ƙara da cewa bayanan da gwamnatin ta fitar na nuna cewa ƴan ta’adda da ƴan bindiga sun zama kamar wata gwamnati mai zaman kanta da ke yarjejeniya, su karɓi kuɗin fansa, su kuma koma cikin daji daga baya su sake sace wasu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp