Home Labarai Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar...

Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar ‘yanci

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, jami’an tsaro sun samu nasarar ceto ɗalibai mata 24 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar sakandiren Maga dake jihar Kebbi a makon da ya gabata.

A ranar 17 ga watan Nuwamba da sanyin safiya ne ‘yan bindigar su ka kai hari makarantar tare da yin garkuwa da ‘yan matan, ‘yan sa’o’i bayan barin dakarun ƙasar daga yankin.

Harin na Kebbi ya ta’azzara matsalar tsaro a Najeriya, inda wasu mahara na daban suka afkawa yankin Eruku na Kwara tare da sace masu ibada kodayake an samu nasarar ceto dukkaninsu.

Haka zalika, Ƙungiyar Kiristocin Najeriya ta ce 50 daga cikin ɗalibai fiye da 300 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar Katolika dake Neja sun shaƙi iskar ‘yanci.

Shugaba Tinubu ya yabawa jami’an tsaron ƙasar da ƙoƙarin da su ke yi, tare da kira na su jajirce don ceto suaran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp