Home Labarai Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar...

Dalibai 24 da ‘yan bindiga suka sace a Kebbi sun shaƙi iskar ‘yanci

Gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa, jami’an tsaro sun samu nasarar ceto ɗalibai mata 24 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar sakandiren Maga dake jihar Kebbi a makon da ya gabata.

A ranar 17 ga watan Nuwamba da sanyin safiya ne ‘yan bindigar su ka kai hari makarantar tare da yin garkuwa da ‘yan matan, ‘yan sa’o’i bayan barin dakarun ƙasar daga yankin.

Harin na Kebbi ya ta’azzara matsalar tsaro a Najeriya, inda wasu mahara na daban suka afkawa yankin Eruku na Kwara tare da sace masu ibada kodayake an samu nasarar ceto dukkaninsu.

Haka zalika, Ƙungiyar Kiristocin Najeriya ta ce 50 daga cikin ɗalibai fiye da 300 da ‘yan bindiga suka sace a makarantar Katolika dake Neja sun shaƙi iskar ‘yanci.

Shugaba Tinubu ya yabawa jami’an tsaron ƙasar da ƙoƙarin da su ke yi, tare da kira na su jajirce don ceto suaran ɗaliban da har yanzu ke hannun ‘yan bindiga.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp