Home General KAROTA ta bukaci Al’ummar jihar Kano su bawa jami’anta hadin kai

KAROTA ta bukaci Al’ummar jihar Kano su bawa jami’anta hadin kai

Hukumar dake lura da zirga-zirgar ababa hawa ta jihar Kano KAROTA ta bukaci direbodin jihar da su zamo masu bin doka da oda, a dukkan lokacin da suke kan titunan jihar.

Mataimakin shugaban hukumar Auwal Lawan Aranposu ne ya bayyana hakan yayin da yake karbar kautar girmamawa da kungiyar shuwagabannin kungiyar direbobin mota ta NURTW shiyyar kano ta kadu ta bashi a dakin taro na hukumar KAROTA dake kano.

Auwal Aranposu ya yabawa kokarin kungiyar na yadda suka ga dacewar bashi wannan kyautar girmama akan yadda yake gudanar da ayyukansa a hukumar.

“Yau ina cike da farin ciki, saboda a ko da yaushe kana gudanar da aikin ka tsakaninka da Allah ba domin wani ya yaba maka ba, sai dan ka sauke nauyin da ke wuyanka, kuma kana gwada adalci da jajircewarka akan aikin dake gabanka, kai dai kasan kan yi ne tsakani da Allah.”

“Ni bana karbar takardar girmama, idan aka ce za’a karramani nakan ce a bari sai na bar kujerar, anan ne za’a gane cewa na cancanta ko kuma akasin haka”

“Amma a dukkan abin da aka lisafta a wannan waje nasan abubuwa ne da idan an yaba min sakamakon yin su na tabbatar da cewa kwarai na aikata su domin ganin an sami gobe mai kyau a harkokin sufurin jihar kano.”

Da yake jawabi tun da fari Shugaban kungiyar shuwa

gabannin kungiyoyin direbobin mota ta NURTW shiyyar kano ta kadu Musa Mika’il, ya yabawa Auwal Aranposu bisa yadda yake kokari wajen kari martaba da mutuncin direbon dake yankin Kano ta Kadu dama jihar kano baki daya.

“Mai girma DMD bazan cika ka da zance ba ina, illa iyaka an sake mika godiyar mu kan yadda kake kare mutuncin direbobin mu, wannan ce ta sanya a madadin su muka ga dacewar karrama ka da wannan lamba ta girma”. Taron ya sami halartar daukacin shuwagabannin kungiyar shuwagabannin direbobi ta NURTW shiyyar kano ta kadu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp