Home Labarai Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda sace ɗalibai a makarantu

Tinubu ya fasa zuwa taron G20 saboda sace ɗalibai a makarantu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya fasa zuwa taron G20 na ƙasashe masu ƙarfin masana’atu a duniya, sakamakon matsalar satar ɗalibai a ƙasar .

Cikin wata sanarwa da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta ce shugaban ya ɗauki matakin ne sakamakon halin da ake ciki a ƙasar na satar ɗalibai a makarantu.

A maimakon haka Shugaba Tinubu ya tura mataimakinsa Kashim Shettima domin ya wakilce shi a taron.

Tun da farko fadar shugaban ƙasar ta ce Tinubu ya ɗage tafiyarsa zuwa taron sakamakon sanin halin da ake ciki game da satar ɗalibai a Kebbi da masu ibada a jihar Kwara.

An tsara gudanar da taron ne a yau Asabar 22 ga watan Nuwamban 2025.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp