Home Labarai Ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace a makarantar Neja –...

Ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace a makarantar Neja – CAN

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), ta ce aƙalla mutum 227, ciki har da ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace lokacin da suka kai hari makarantar St. Mary da ke garin Papiri a jihar Neja.

Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar ta CAN reshen jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna ya fitar ya ce harin ya jefa al’ummar yankin cikin ɗimuwa da kaɗuwa.

Da tsakar daren ranar Alhamis ne wasu mahara ɗauke da makamai suka far wa makarantar – wadda ta kwana ce, da ta ƙunshi furamare da sakandire – tare da sace ɗaliban, bayan da suka harbi maigadi.

Gwamnatin jihar Neja ta ce sai da bayar da umarnin rufe duka makarantun yankin sakamakon samun bayanan sirri kan barazanar tsaro, amma makarantar ta yi gaban kanta wajen buɗewa tare da ci gaba da karatu ba tare da neman izini ko sanar da gwamnati ba.

Harin na zuwa ƙasa da mako guda da wasu ƴanbidiga suka sace ɗalibai mata 25 a makarantar sakandiren ƴanmata da ke garin Maga a jihar Kebbi mai maƙwabtaka.

Tuni dai gwamnatin ƙasar ta ce ta baza jami’an tsaro domin kuɓutar da duka ɗaliban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp