Home Labarai Ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace a makarantar Neja –...

Ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace a makarantar Neja – CAN

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), ta ce aƙalla mutum 227, ciki har da ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace lokacin da suka kai hari makarantar St. Mary da ke garin Papiri a jihar Neja.

Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar ta CAN reshen jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna ya fitar ya ce harin ya jefa al’ummar yankin cikin ɗimuwa da kaɗuwa.

Da tsakar daren ranar Alhamis ne wasu mahara ɗauke da makamai suka far wa makarantar – wadda ta kwana ce, da ta ƙunshi furamare da sakandire – tare da sace ɗaliban, bayan da suka harbi maigadi.

Gwamnatin jihar Neja ta ce sai da bayar da umarnin rufe duka makarantun yankin sakamakon samun bayanan sirri kan barazanar tsaro, amma makarantar ta yi gaban kanta wajen buɗewa tare da ci gaba da karatu ba tare da neman izini ko sanar da gwamnati ba.

Harin na zuwa ƙasa da mako guda da wasu ƴanbidiga suka sace ɗalibai mata 25 a makarantar sakandiren ƴanmata da ke garin Maga a jihar Kebbi mai maƙwabtaka.

Tuni dai gwamnatin ƙasar ta ce ta baza jami’an tsaro domin kuɓutar da duka ɗaliban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp