Home Labarai Ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace a makarantar Neja –...

Ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace a makarantar Neja – CAN

Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), ta ce aƙalla mutum 227, ciki har da ɗalibai 215 da malamai 12 ƴanbindiga suka sace lokacin da suka kai hari makarantar St. Mary da ke garin Papiri a jihar Neja.

Cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar ta CAN reshen jihar Neja, Most Rev. Bulus Dauwa Yohanna ya fitar ya ce harin ya jefa al’ummar yankin cikin ɗimuwa da kaɗuwa.

Da tsakar daren ranar Alhamis ne wasu mahara ɗauke da makamai suka far wa makarantar – wadda ta kwana ce, da ta ƙunshi furamare da sakandire – tare da sace ɗaliban, bayan da suka harbi maigadi.

Gwamnatin jihar Neja ta ce sai da bayar da umarnin rufe duka makarantun yankin sakamakon samun bayanan sirri kan barazanar tsaro, amma makarantar ta yi gaban kanta wajen buɗewa tare da ci gaba da karatu ba tare da neman izini ko sanar da gwamnati ba.

Harin na zuwa ƙasa da mako guda da wasu ƴanbidiga suka sace ɗalibai mata 25 a makarantar sakandiren ƴanmata da ke garin Maga a jihar Kebbi mai maƙwabtaka.

Tuni dai gwamnatin ƙasar ta ce ta baza jami’an tsaro domin kuɓutar da duka ɗaliban.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp