Home General NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC, ya tabbatar da fashewar da ta faru a ranar Laraba a wasu al’ummomi biyu da ke kusa da masarautar Gbaramatu ta jihar Delta mai arziƙin mai.

A wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Alhamis da yamma, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin fashewar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike.

NNPC ba ta bayyana adadin lalacewar da ta faru ko asarar rayuka.

Kamfanin ya ce an ƙaddamar da matakan gaggawa tare da haɗa kai da hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin ɗaukar matakan da suka dace.

“Abu mafi muhimmanci a wannan lokaci shi ne kare rayukan al’ummomin da ke kusa da wurin da kuma kiyaye muhalli,” in ji jami’in hulda da jama’a na NNPC, Andy Odeh.

NNPC ta bayyana cewa an gano raguwar ƙarfi a daya daga cikin manyan bututunta, wanda ke nuna yiwuwar fitar mai, lamarin da ya sa aka fara binciken farko.

Fashewar bututun mai ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda kungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ko masu satar mai ke yawan lalata bututun domin sace man fetur.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp