Home General NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC, ya tabbatar da fashewar da ta faru a ranar Laraba a wasu al’ummomi biyu da ke kusa da masarautar Gbaramatu ta jihar Delta mai arziƙin mai.

A wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Alhamis da yamma, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin fashewar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike.

NNPC ba ta bayyana adadin lalacewar da ta faru ko asarar rayuka.

Kamfanin ya ce an ƙaddamar da matakan gaggawa tare da haɗa kai da hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin ɗaukar matakan da suka dace.

“Abu mafi muhimmanci a wannan lokaci shi ne kare rayukan al’ummomin da ke kusa da wurin da kuma kiyaye muhalli,” in ji jami’in hulda da jama’a na NNPC, Andy Odeh.

NNPC ta bayyana cewa an gano raguwar ƙarfi a daya daga cikin manyan bututunta, wanda ke nuna yiwuwar fitar mai, lamarin da ya sa aka fara binciken farko.

Fashewar bututun mai ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda kungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ko masu satar mai ke yawan lalata bututun domin sace man fetur.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp