Home General NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPC, ya tabbatar da fashewar da ta faru a ranar Laraba a wasu al’ummomi biyu da ke kusa da masarautar Gbaramatu ta jihar Delta mai arziƙin mai.

A wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Alhamis da yamma, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin fashewar ba, kuma ana ci gaba da gudanar da bincike.

NNPC ba ta bayyana adadin lalacewar da ta faru ko asarar rayuka.

Kamfanin ya ce an ƙaddamar da matakan gaggawa tare da haɗa kai da hukumomin tsaro da shugabannin al’umma domin ɗaukar matakan da suka dace.

“Abu mafi muhimmanci a wannan lokaci shi ne kare rayukan al’ummomin da ke kusa da wurin da kuma kiyaye muhalli,” in ji jami’in hulda da jama’a na NNPC, Andy Odeh.

NNPC ta bayyana cewa an gano raguwar ƙarfi a daya daga cikin manyan bututunta, wanda ke nuna yiwuwar fitar mai, lamarin da ya sa aka fara binciken farko.

Fashewar bututun mai ba sabon abu ba ne a Najeriya, inda kungiyoyin masu tayar da ƙayar baya ko masu satar mai ke yawan lalata bututun domin sace man fetur.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp