Home Labarai Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a...

Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da kafa Runduna ta Musamman (Special Task Force) domin magance barazanar tsaro a tashoshin mota da sauran muhimman wuraren taruwar jama’a a fadin jihar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi. Sanarwar ta ce matakin na nuna kudurin gwamnati na hana kutsen masu aikata laifi, musamman a wuraren shiga da fita na birnin Kano.

An bayyana tashoshin mota a matsayin wuraren da ke da hadarin tsaro, sakamakon yawaitar zirga-zirga da kuma kamun wasu da ake zargi da aikata laifi a tashar mota ta Kofar Ruwa kwanan nan.

Rundunar za ta gudanar da sa ido, tattara bayanan sirri da hadin gwiwar ayyukan tsaro a tashoshin mota, gidajen mai da sauran wuraren jama’a, domin dakile barazana tun kafin ta tsananta. Gwamnan ya jaddada manufar gwamnatinsa ta ba da cikakken goyon baya ga hukumomin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp