Home Labarai Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a...

Gwamnan Kano Ya Kafa Runduna ta Musamman Don Tabbatar da Tsaro a Tashoshin Mota

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya amince da kafa Runduna ta Musamman (Special Task Force) domin magance barazanar tsaro a tashoshin mota da sauran muhimman wuraren taruwar jama’a a fadin jihar.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Lahadi. Sanarwar ta ce matakin na nuna kudurin gwamnati na hana kutsen masu aikata laifi, musamman a wuraren shiga da fita na birnin Kano.

An bayyana tashoshin mota a matsayin wuraren da ke da hadarin tsaro, sakamakon yawaitar zirga-zirga da kuma kamun wasu da ake zargi da aikata laifi a tashar mota ta Kofar Ruwa kwanan nan.

Rundunar za ta gudanar da sa ido, tattara bayanan sirri da hadin gwiwar ayyukan tsaro a tashoshin mota, gidajen mai da sauran wuraren jama’a, domin dakile barazana tun kafin ta tsananta. Gwamnan ya jaddada manufar gwamnatinsa ta ba da cikakken goyon baya ga hukumomin tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp