Home General Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a...

Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna

Soji

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na operation enduring peace sun lalata wata maɓoyar masu garkuwa da mutane tare da ceto mutum takwas a dajin Badurum Kasa da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna

Rundunar ta ce sojojin sun samu wannan nasarar ne a yayin wani samame da suka kai a wurin maɓoyar.

Samamen ya gudana ne a ranar 28 ga Janairun 2026, bayan samun sahihin bayanan sirri kan inda masu laifin ke ɓoye.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar, sojojin sun kai samamennne cikin gaggawa tare da haɗin gwiwar rundunar ƴansandan Zango Kataf da dakarun sa kai ta CJTF da masu gadin daji da kuma mafarauta inda suka kutsa cikin dajin domin kama masu garkuwar.

Sojojin sun yi arangama da masu garkuwa da mutanen inda wasu suka tsere suka bar waɗanda suka sace a baya lamarin da ya sa sojojin suka yi nasarar ceto mutane takwas.

An haɗa mutanen da aka ceto su da iyalansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp