Home General Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a...

Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna

Soji

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojinta na operation enduring peace sun lalata wata maɓoyar masu garkuwa da mutane tare da ceto mutum takwas a dajin Badurum Kasa da ke ƙaramar hukumar Kauru a jihar Kaduna

Rundunar ta ce sojojin sun samu wannan nasarar ne a yayin wani samame da suka kai a wurin maɓoyar.

Samamen ya gudana ne a ranar 28 ga Janairun 2026, bayan samun sahihin bayanan sirri kan inda masu laifin ke ɓoye.

A cewar sanarwar da rundunar ta fitar, sojojin sun kai samamennne cikin gaggawa tare da haɗin gwiwar rundunar ƴansandan Zango Kataf da dakarun sa kai ta CJTF da masu gadin daji da kuma mafarauta inda suka kutsa cikin dajin domin kama masu garkuwar.

Sojojin sun yi arangama da masu garkuwa da mutanen inda wasu suka tsere suka bar waɗanda suka sace a baya lamarin da ya sa sojojin suka yi nasarar ceto mutane takwas.

An haɗa mutanen da aka ceto su da iyalansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp