Home Labarai Sojoji sun jagoranci mayar da ƴan gudun hijirar Najeriya gida daga Kamaru

Sojoji sun jagoranci mayar da ƴan gudun hijirar Najeriya gida daga Kamaru

Rundunar Sojin Najeriya a karkashin operation haɗin kai ta sanar da jagorantar dawowar ‘yan gudun hijirar Najeriya daga Jamhuriyar Kamaru zuwa Jihar Borno cikin tsaro.

A cewar sanarwar da ta fitar, a ranar 27 ga Janairu, 2026, sojojin tare da hadin gwiwar dakarun ƴan sa kai ta CJTF da ‘yan banga na gari sun samar da cikakken tsaro yayin da ‘yan gudun hijirar ke ƙetare iyaka daga Kirawa zuwa garin Pulka a ƙaramar hukumar Gwoza.

Wasu daga cikin wadanda suka dawo sun shafe sama da shekaru 11 a gudun hijira sakamakon rikicin ‘yan ta’adda.

Aikin dawo da ‘yan gudun hijirar ya fara ne daga Minawawu a Kamaru zuwa Moruwa kafin shiga Kirawa a Najeriya.

An gudanar da aikin bisa ƙa’idojin jin kai da tsaro, tare da hadin gwiwar Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Kasa da gwamnatin jihar Borno da sauran hukumomin tsaro.

Wata babbar tawaga daga gwamnatin jihar karkashin jagorancin Wakilbe, wakilin gwamna Babagana Umara Zulum, ta halarci taron tare da wakilan UNHCR da IOM.

Kwamandan dakarun ƴan sa-kai ta CJTF, Birgediya Janar Nasiru Abdullahi ne ya tarbe su kafin a raka su zuwa cibiyar karɓar baƙi a Pulka.

A can ne aka yi musu rijista inda aka raba musu tallafi da suka hada da kuɗade da tabarma da gado daga gwamnatin Borno da kayan abinci daga gwamnatin tarayya, da kuma tallafin kudi daga UNHCR.

Rundunar Sojin ta tabbatar da cewa aikin ya gudana lafiya ba tare da wata matsala ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp