Home General Kotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zanga

Kotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zanga

Kotun warware matsalolin ma’aikata ta ƙasa ta bayar da umarnin wucin-gadi da ke hana manyan ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya, ciki har da NLC da TUC, tare da wasu ƙungiyoyi uku, yin yajin aiki ko zanga-zangar da suka shirya farawa.

Mai shari’a Emmanuel Subilim ne ya bayar da umarnin a birnin Abuja, bayan sauraron buƙatar gaggawa da Ministan Babban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike, tare da hukumar ma’aikatan babban birnin tarayya FCTA suka shigar.

Alƙalin ya umurci waɗanda ake ƙara, tare da wakilansu ko jami’ansu, da su dakatar da duk wani nau’i na yajin aiki ko zanga-zanga har zuwa lokacin da za a saurari buƙatar da aka gabatar.

Haka kuma, kotun ta umurci hukumomin tsaro da ke cikin ƙarar da su tabbatar da cewa an kiyaye doka da oda, tare da hana duk wani rikici a Babban Birnin Tarayya.

Lauyan da ke wakiltar minista Wike da FCTA, Ogwu Onoja, ya shaida wa kotu cewa shugaban ƙungiyar ƙadago ya fitar da wata sanarwar tattara mambobi da ƙungiyoyin haɗin gwiwa domin shirya babbar zanga-zanga a ranar 3 ga Fabrairu, lamarin da ya ce ya saɓa wa umarnin kotu.

Sanarwar, wadda shugabannin ƙungiyoyin biyu suka rattaɓa wa hannu, ta umurci ma’aikatan da ke yajin aiki da su ci gaba, bisa hujjar cewa lauyansu, Femi Falana, ya shigar da ƙara zuwa kotun ɗaukaka ƙara kan hukuncin wucin-gadin da kotu ta yanke.

Haka kuma, an ce haɗakar ƙungiyar ƴan ƙwadago ta JUAC ta fitar da wata sanarwa da ke umartar dukkan ma’aikata da su ci gaba da yajin aikin, matakin da ɓangaren masu ƙara suka ce na iya haddasa rushewar doka da oda a Babban Birnin Ƙasa.

Kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 10 ga Fabrairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp