Home General Kotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zanga

Kotu ta hana ƙungiyoyin ƙwadago yin yajin aiki ko zanga-zanga

Kotun warware matsalolin ma’aikata ta ƙasa ta bayar da umarnin wucin-gadi da ke hana manyan ƙungiyoyin ƙwadago a Najeriya, ciki har da NLC da TUC, tare da wasu ƙungiyoyi uku, yin yajin aiki ko zanga-zangar da suka shirya farawa.

Mai shari’a Emmanuel Subilim ne ya bayar da umarnin a birnin Abuja, bayan sauraron buƙatar gaggawa da Ministan Babban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike, tare da hukumar ma’aikatan babban birnin tarayya FCTA suka shigar.

Alƙalin ya umurci waɗanda ake ƙara, tare da wakilansu ko jami’ansu, da su dakatar da duk wani nau’i na yajin aiki ko zanga-zanga har zuwa lokacin da za a saurari buƙatar da aka gabatar.

Haka kuma, kotun ta umurci hukumomin tsaro da ke cikin ƙarar da su tabbatar da cewa an kiyaye doka da oda, tare da hana duk wani rikici a Babban Birnin Tarayya.

Lauyan da ke wakiltar minista Wike da FCTA, Ogwu Onoja, ya shaida wa kotu cewa shugaban ƙungiyar ƙadago ya fitar da wata sanarwar tattara mambobi da ƙungiyoyin haɗin gwiwa domin shirya babbar zanga-zanga a ranar 3 ga Fabrairu, lamarin da ya ce ya saɓa wa umarnin kotu.

Sanarwar, wadda shugabannin ƙungiyoyin biyu suka rattaɓa wa hannu, ta umurci ma’aikatan da ke yajin aiki da su ci gaba, bisa hujjar cewa lauyansu, Femi Falana, ya shigar da ƙara zuwa kotun ɗaukaka ƙara kan hukuncin wucin-gadin da kotu ta yanke.

Haka kuma, an ce haɗakar ƙungiyar ƴan ƙwadago ta JUAC ta fitar da wata sanarwa da ke umartar dukkan ma’aikata da su ci gaba da yajin aikin, matakin da ɓangaren masu ƙara suka ce na iya haddasa rushewar doka da oda a Babban Birnin Ƙasa.

Kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 10 ga Fabrairu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp