Home Labarai Gwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jihar

Gwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jihar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kano SEMA, ta sanar da cewa za ta ci gaba da kwashe masu matsalolin lafiyar kwakwalwa daga titunan birnin da kewaye.

Bayanai na cewa akwai ɗumbin masu fama da wannan matsala da ke yawo a titunan birnin Kano, cikin mawuycin hali lamarin da ke ƙara matsalar tsaro.

Hukumar ta SEMA ta ce za ta killace su tare da basu magani, kafin a mayar da su garuruwansu.

Hukumar ta kuma ce gwmnatin Kano ta bijiro da aikin kwashe masu larurar kwakwalwar ne domin a basu kulawar da ta dace a matsayinsu na ‘yanadam tare da saita musu rayuwa don su koma cikin iyalansu.

Babban sakataren hukumar, Abdullahi Isyaku Kubarachi, ya shaida wa manema labarai cewa wannan aiki da suka fara dama yana cikin aikace-aikacensu, inda yace hukumar ta gudanar da aikin ne da dadddare da hadin gwiwar wasu hukumomin tsaro, a wasu kananan hukumomin birnin Kano hudu.

Kubarachi ya ƙara da cewa umarnin da gwamnatin Kano ta basu, shi ne su gudanar da aikin tattara masu matsalar kwakwalwar a ƙananan hukumomin cikin birnin Kano tukuna, sannan yace aikin zai taimaka wajen magance matsalar tsaro.

Sakataren hukumar ta SEMA yace mutanen da basu gamsu da bayanansu ba, saboda sha’anin tsaro su mika su ga jami’an tsaro.

Bayanai na cewa masu matsalar kwakwalwa dai suna fama da matsalolin rayuwa a yankunan Najeriya da dama, inda da dama daga cikinsu, matsalar kwakwalwar ba ta yi tsamari ba, amma saboda rashin kulawa da kuma tsangwama suke ta’azzara halin da suke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp