Home Labarai Gwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jihar

Gwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jihar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kano SEMA, ta sanar da cewa za ta ci gaba da kwashe masu matsalolin lafiyar kwakwalwa daga titunan birnin da kewaye.

Bayanai na cewa akwai ɗumbin masu fama da wannan matsala da ke yawo a titunan birnin Kano, cikin mawuycin hali lamarin da ke ƙara matsalar tsaro.

Hukumar ta SEMA ta ce za ta killace su tare da basu magani, kafin a mayar da su garuruwansu.

Hukumar ta kuma ce gwmnatin Kano ta bijiro da aikin kwashe masu larurar kwakwalwar ne domin a basu kulawar da ta dace a matsayinsu na ‘yanadam tare da saita musu rayuwa don su koma cikin iyalansu.

Babban sakataren hukumar, Abdullahi Isyaku Kubarachi, ya shaida wa manema labarai cewa wannan aiki da suka fara dama yana cikin aikace-aikacensu, inda yace hukumar ta gudanar da aikin ne da dadddare da hadin gwiwar wasu hukumomin tsaro, a wasu kananan hukumomin birnin Kano hudu.

Kubarachi ya ƙara da cewa umarnin da gwamnatin Kano ta basu, shi ne su gudanar da aikin tattara masu matsalar kwakwalwar a ƙananan hukumomin cikin birnin Kano tukuna, sannan yace aikin zai taimaka wajen magance matsalar tsaro.

Sakataren hukumar ta SEMA yace mutanen da basu gamsu da bayanansu ba, saboda sha’anin tsaro su mika su ga jami’an tsaro.

Bayanai na cewa masu matsalar kwakwalwa dai suna fama da matsalolin rayuwa a yankunan Najeriya da dama, inda da dama daga cikinsu, matsalar kwakwalwar ba ta yi tsamari ba, amma saboda rashin kulawa da kuma tsangwama suke ta’azzara halin da suke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp