Home Labarai Gwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jihar

Gwamnatin Kano ta fara kwashe masu larurar ƙwaƙwalwa daga titunan jihar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Kano SEMA, ta sanar da cewa za ta ci gaba da kwashe masu matsalolin lafiyar kwakwalwa daga titunan birnin da kewaye.

Bayanai na cewa akwai ɗumbin masu fama da wannan matsala da ke yawo a titunan birnin Kano, cikin mawuycin hali lamarin da ke ƙara matsalar tsaro.

Hukumar ta SEMA ta ce za ta killace su tare da basu magani, kafin a mayar da su garuruwansu.

Hukumar ta kuma ce gwmnatin Kano ta bijiro da aikin kwashe masu larurar kwakwalwar ne domin a basu kulawar da ta dace a matsayinsu na ‘yanadam tare da saita musu rayuwa don su koma cikin iyalansu.

Babban sakataren hukumar, Abdullahi Isyaku Kubarachi, ya shaida wa manema labarai cewa wannan aiki da suka fara dama yana cikin aikace-aikacensu, inda yace hukumar ta gudanar da aikin ne da dadddare da hadin gwiwar wasu hukumomin tsaro, a wasu kananan hukumomin birnin Kano hudu.

Kubarachi ya ƙara da cewa umarnin da gwamnatin Kano ta basu, shi ne su gudanar da aikin tattara masu matsalar kwakwalwar a ƙananan hukumomin cikin birnin Kano tukuna, sannan yace aikin zai taimaka wajen magance matsalar tsaro.

Sakataren hukumar ta SEMA yace mutanen da basu gamsu da bayanansu ba, saboda sha’anin tsaro su mika su ga jami’an tsaro.

Bayanai na cewa masu matsalar kwakwalwa dai suna fama da matsalolin rayuwa a yankunan Najeriya da dama, inda da dama daga cikinsu, matsalar kwakwalwar ba ta yi tsamari ba, amma saboda rashin kulawa da kuma tsangwama suke ta’azzara halin da suke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp