Home Labarai Babu gudu ba ja da baya kan zanga-zanga a Abuja – NLC

Babu gudu ba ja da baya kan zanga-zanga a Abuja – NLC

Ƙungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC a Najeriya, sun ce suna nan daram kan ƙudirinsu na gudanar da zanga-zangar da suka shirya yi a gobe Talata.

Sun ce za su yi zanga-zangar ne domin nuna goyon bayansu ga ma’aikatan Hukumar Raya Babban Birnin Ƙasar Abuja, waɗanda ke neman a biya musu buƙatunsu.

Ƙungiyoyin na NLC da TUC sun umarci dukkan rassansu da majalisun jihohi a yankin na Abuja da ƙewaye, da su tabbatar sun halarci zanga-zangar lumana da doka ta amince da ita, wadda aka tsara za ta yi ranar Talata.

Wannan na zuwa ne duk da cewa rundunar ƴansandan Abuja ta shawarci ƙungiyoyin ƙwadagon da su dakatar da zanga-zangar, bisa dalilan tsaro.

Sai dai, sakataren tsare-tsare na ƙungiyar ta NLC, Nasir Kabir, ya shaida wa BBC cewa ba su da niyyar sauya matsaya kan ƙudirinsu na gudanar da zanga-zangar.

“Zanga-zanga ce ta lumana da nuna fushi da ma’aikata za su yi kan zalunci na wannan mutumi wanda yake ganin ya fi ƙarfin kowa. Mu dai bai fi ƙarfin mu ba, muna bayan ma’aikata.

“Idan ba a biya ma’aikata hakkokinsu ba da alawus-alawus da kuma inganta aikinsu ba, yajin aiki yanzu muka fara babu wanda zai janye,” in ji Nasir Kabir.

Rahotanni na nuna cewa ma’aikatan hukumar gudanarwar babban birnin Abuja, sun shiga yajin aikin sai baba-ta-gani tun a ranar 19 ga watan Janairun da ya gabata, bisa zargin rashin biyan albashi, da rashin ƙarin girma da kuma lalacewar yanayin aiki.

Lamarin ya sa hukumar FCDA ta garzaya kotun masana’antu ta ƙasar, inda ta bayyana yajin aikin a matsayin wanda bai halatta ba tare da neman kotun ta hana ma’aikatan yajin aikin, sai dai kungiyoyin NLC da TUC sun sha alwashin tsayawa kai da fata wajen ƙwatowa ma’aikatan hakkokin su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp