Home Labarai Yadda gobara ta ƙona shaguna 25 da Kanti 19 a Kano

Yadda gobara ta ƙona shaguna 25 da Kanti 19 a Kano

Akalla shaguna 25 da Katina 19 ne a ka tabbatar sun kone a babbar Kasuwar Singa da ke a birnin Kano a arewacin tarayyar Najeriya.

Mai magana da yawun hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Abdullahi ne ya tabbatar da haka a wata rubutacciyar sanarwa.

Hukumomi a Kano dai sun bayyana cewar gobarar da haddasa hasarar kaya  na miliyoyin Naira kamin daga bisani a ka samu nasarar kashe Wutar.

Wutar ta tashi ne da misalin karfe 5 na Asubah kuma daga nan ne mutane su ka nemi agajin gaggawa daga hukumar kashe gobara ta jihar abin da ya takaita matsalar da kuma kare akalla shaguna 24 daga konewa.

Matsalolin hanya da ke da nasaba da manyanyan Motocin dakon kaya da ake ajiyewa a wurin cikin kasuwar na daga cikin matsalolin da su ka ta’azzara matsalar.

Wutar ta samo asali ne daga wayoyin Wutar lantarki a daya daga cikin shagunan da su ka kone, saidai ba a samu rasa rayka ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp