Home General Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe

Gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe

Wata mummunar gobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar Yobe inda ta ƙone wani ɓangare na kasuwar da ke arewa maso yammacin Najeriya.

Gobarar ta lalata rumfuna a kasuwar wadda ke hada-hada mako-mako, lamarin da ya jefa, ɗimbin mutanen da suka dogara da kasuwar wajen harkokin rayuwarsu cikin mawuyacin hali.

Gobarar dai ta tashi ne jiya da yamma daf da lokacin buɗa bakin azumin ramadan, inda ta mamaye rumfuna 135 wadanda aƙasarinsu na kwano da katako ne wasu kuma na itace da kara.

Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Yobe, Dr. Muhammad Goje ya tabbatar da aukuwar wannan gobara.

Ya ƙara da cewa gobarar ba ta shiga shaguna ba kuma ba a rasa rai ko ɗaya ,a a gobarar.

Dr Muhammad Goje ya ƙara da cewa wannan tashin gobara a kasuwar Fika itace ta uku da aka samu a kasuwanni daban-daban cikin kasa da wata daya a jihar ciki harda kasuwar Bukarti, inda rumfuna kusan dari suka ƙone, sai kuma kasuwar Fuchimiran a ƙaramar hukumar Geidam, inda rufunan da gidajen mutane da dama suka kone.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp