Home Labarai Ba mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba – Gwamnatin Najeriya

Ba mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba – Gwamnatin Najeriya

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ba ta taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba ko nuna wariyar addini ba, bayan rahoton bincike kan zargin muzgunawa da kashe Kiristoci da Majalisar Wakilan Amurka ta fitar.

Gwamnatin ta ce “duk da ƙalubalen tsaro da wasu yankuna ke fuskanta, matsalolin sun samo asali ne daga ta’addanci da fashi da makami, da rikice-rikicen al’umma.”

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwar da ya fitr a ranar Talata, inda ya ce ƙundin tsarin mulkin ƙasa ya tanadi ‘yancin addini da ibada ga kowane dan kasa, kuma gwamnati na nan daram wajen kare waɗannan haƙƙoƙi da tabbatar da adalci ga kowa.

Ministan ya ƙara da cewa “gwamnati ta ƙarfafa ayyukan haɗin gwiwar jami’an tsaro a yankunan da matsalar ta fi ƙamari, tare da fadada farmakin yaki da ta’addanci da lalata hanyoyin masu garkuwa da mutane, da kuma kama manyan masu aikata laifi.”

Haka kuma gwamnatin Najeriya ta inganta haɗin gwiwar hukumomi domin saurin ɗaukar mataki musamman a yankunan karkara masu rauni in ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma jaddada muhimmancin dangantaka tsakanin Najeriya da Amurka, tana mai cewa ƙasar na maraba da tattaunawa da haɗin kai bisa mutunta juna da mutunta ikon ƙasashe.

Ta ce gwamnati za ta ci gaba da aiki da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa ta hanyoyin diflomasiyya yayin da take mai da hankali kan babban nauyinta na kare rayuka da dukiyoyin dukkan ‘yan kasa.

A jiya ne ƴan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da rahoto ga shugaban Amurka Donald Trump kan binciken da suka kammala game da zargin cin zarafin Kiristoci da musguna musu a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp