Home Labarai Ba mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba – Gwamnatin Najeriya

Ba mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba – Gwamnatin Najeriya

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ba ta taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba ko nuna wariyar addini ba, bayan rahoton bincike kan zargin muzgunawa da kashe Kiristoci da Majalisar Wakilan Amurka ta fitar.

Gwamnatin ta ce “duk da ƙalubalen tsaro da wasu yankuna ke fuskanta, matsalolin sun samo asali ne daga ta’addanci da fashi da makami, da rikice-rikicen al’umma.”

Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a wata sanarwar da ya fitr a ranar Talata, inda ya ce ƙundin tsarin mulkin ƙasa ya tanadi ‘yancin addini da ibada ga kowane dan kasa, kuma gwamnati na nan daram wajen kare waɗannan haƙƙoƙi da tabbatar da adalci ga kowa.

Ministan ya ƙara da cewa “gwamnati ta ƙarfafa ayyukan haɗin gwiwar jami’an tsaro a yankunan da matsalar ta fi ƙamari, tare da fadada farmakin yaki da ta’addanci da lalata hanyoyin masu garkuwa da mutane, da kuma kama manyan masu aikata laifi.”

Haka kuma gwamnatin Najeriya ta inganta haɗin gwiwar hukumomi domin saurin ɗaukar mataki musamman a yankunan karkara masu rauni in ji sanarwar.

Sanarwar ta kuma jaddada muhimmancin dangantaka tsakanin Najeriya da Amurka, tana mai cewa ƙasar na maraba da tattaunawa da haɗin kai bisa mutunta juna da mutunta ikon ƙasashe.

Ta ce gwamnati za ta ci gaba da aiki da abokan hulɗar ƙasa da ƙasa ta hanyoyin diflomasiyya yayin da take mai da hankali kan babban nauyinta na kare rayuka da dukiyoyin dukkan ‘yan kasa.

A jiya ne ƴan majalisar wakilan Amurka suka gabatar da rahoto ga shugaban Amurka Donald Trump kan binciken da suka kammala game da zargin cin zarafin Kiristoci da musguna musu a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp