Home Labarai DSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a...

DSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a Edo

Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS sun kama mutum na shida da ake zargi da hannu a kitsa harin da aka kai a cocin Katolik na St. Francis da ke Owo a jihar Edo a shekarar 2022, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fiye da masu ibada 40 tare da jikkata wasu da dama kamar yadda gidan talabijin na gwamnati NTA ya ruwaito.

Tun da farko, hukumar ta riga ta kama mutum 5 da, inda suke fuskantar shari’ar aikata laifukan ta’addanci, yayin da mutum na shida da aka kama na baya-bayan nan, mai suna Sani Yusuf, ya shafe kusan shekara huɗu yana ɓuya kafin a kama shi a wata unguwa mai suna Iguosa da ke ƙaramar hukumar Ovia North Local Government Area a jihar Edo.

Wata majiyar tsaro ta bayyana cewa Yusuf wani babban kwamanda ne a ƙungiyar ISWAP kuma bayan harin Owo ya tsere zuwa Kano kafin daga bisani ya koma ɓuya a yankin na Edo.

Rahotanni sun ce ya amsa laifin yana da hannu a harin da aka kai cocin da kuma wasu hare-haren ƙungiyar, ciki har da farmakin da aka kai a barikin sojoji na Suleja a watan Yulin 2022 da kuma sace-sacen mutane a Kaduna da kewaye.

“Ya kuma amince yana da hannu a harin da aka kai a shinge sojoji na Zuma Rock kusa da Suleja, wanda ya yi sanadin mutuwar sojoji biyar, tare da bayyana cewa ya taɓa aiki a ƙarƙashin wani babban jagoran ƙungiyar mai suna Abu Ikirimah wanda aka kama a 2024.” in ji majiyar kamar yadda NTA ta ruwaito.

Jami’an tsaro sun ce kama Yusuf wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin tabbatar da adalci ga waɗanda harin ya rutsa da su, da kuma kara tabbatar da yaki da ta’addanci a fadin Najeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp