Home Labarai DSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a...

DSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a Edo

Jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS sun kama mutum na shida da ake zargi da hannu a kitsa harin da aka kai a cocin Katolik na St. Francis da ke Owo a jihar Edo a shekarar 2022, wanda ya yi sanadiyar mutuwar fiye da masu ibada 40 tare da jikkata wasu da dama kamar yadda gidan talabijin na gwamnati NTA ya ruwaito.

Tun da farko, hukumar ta riga ta kama mutum 5 da, inda suke fuskantar shari’ar aikata laifukan ta’addanci, yayin da mutum na shida da aka kama na baya-bayan nan, mai suna Sani Yusuf, ya shafe kusan shekara huɗu yana ɓuya kafin a kama shi a wata unguwa mai suna Iguosa da ke ƙaramar hukumar Ovia North Local Government Area a jihar Edo.

Wata majiyar tsaro ta bayyana cewa Yusuf wani babban kwamanda ne a ƙungiyar ISWAP kuma bayan harin Owo ya tsere zuwa Kano kafin daga bisani ya koma ɓuya a yankin na Edo.

Rahotanni sun ce ya amsa laifin yana da hannu a harin da aka kai cocin da kuma wasu hare-haren ƙungiyar, ciki har da farmakin da aka kai a barikin sojoji na Suleja a watan Yulin 2022 da kuma sace-sacen mutane a Kaduna da kewaye.

“Ya kuma amince yana da hannu a harin da aka kai a shinge sojoji na Zuma Rock kusa da Suleja, wanda ya yi sanadin mutuwar sojoji biyar, tare da bayyana cewa ya taɓa aiki a ƙarƙashin wani babban jagoran ƙungiyar mai suna Abu Ikirimah wanda aka kama a 2024.” in ji majiyar kamar yadda NTA ta ruwaito.

Jami’an tsaro sun ce kama Yusuf wani gagarumin ci gaba ne a ƙoƙarin tabbatar da adalci ga waɗanda harin ya rutsa da su, da kuma kara tabbatar da yaki da ta’addanci a fadin Najeriya

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp