Home Labarai Yadda Lakurawa suka kashe masallata a Kebbi

Yadda Lakurawa suka kashe masallata a Kebbi

'Yan Ta'adda

Kamfanin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa aƙalla masallata biyar ne suka mutu yayin da wasu uku kuma suka jikkata a wani harin ramuwar gayya da mayaƙan Lakurawa suka kai a masallaci a jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya, a daren Laraba.

Lakurawan sun buɗe wuta a masallacin dake ƙauyen Dadin Kowa a ƙaramar hukumar Maiyama yayin da masallata ke gudanar da sallar tarawihi a wata mai tsarki ta Ramadan.

Wani rahoton tsaro da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu ya ce an kashe mutane goma a harin.

Kakakin ‘yan sandan Kebbi, Bashir Usman, bai amsa buƙatar AFP na ƙarin bayani ba nan take, amma ya shaida wa NAN cewa harin ya biyo bayan kashe wasu daga cikin mayakan Lakurawa a wani “yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan jirgin soji.

Usman ya ce: “Harin na ramuwar gayya ne daga wasu yanbindiga da ake zargin ƴan kungiyar Lakurawa ne, bayan wani yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan rundunar sojin Najeriya.”

An danganta Lakurawa da kai hare-hare da dama a al’ummomin arewacin jihar Kebbi da jihar Sokoto dake makwabta.

Yan kungiyar na kai hare-hare daga sansanin su a cikin daji tare da satar dabbobi da kuma tilastawa mazauna biyan haraji.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp