Home Labarai Yadda Lakurawa suka kashe masallata a Kebbi

Yadda Lakurawa suka kashe masallata a Kebbi

'Yan Ta'adda

Kamfanin Labarai na Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa aƙalla masallata biyar ne suka mutu yayin da wasu uku kuma suka jikkata a wani harin ramuwar gayya da mayaƙan Lakurawa suka kai a masallaci a jihar Kebbi da ke arewacin Najeriya, a daren Laraba.

Lakurawan sun buɗe wuta a masallacin dake ƙauyen Dadin Kowa a ƙaramar hukumar Maiyama yayin da masallata ke gudanar da sallar tarawihi a wata mai tsarki ta Ramadan.

Wani rahoton tsaro da kamfanin dillancin labarai na AFP ya samu ya ce an kashe mutane goma a harin.

Kakakin ‘yan sandan Kebbi, Bashir Usman, bai amsa buƙatar AFP na ƙarin bayani ba nan take, amma ya shaida wa NAN cewa harin ya biyo bayan kashe wasu daga cikin mayakan Lakurawa a wani “yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan jirgin soji.

Usman ya ce: “Harin na ramuwar gayya ne daga wasu yanbindiga da ake zargin ƴan kungiyar Lakurawa ne, bayan wani yunƙurin kautan ɓauna da bai yi nasara ba a kan rundunar sojin Najeriya.”

An danganta Lakurawa da kai hare-hare da dama a al’ummomin arewacin jihar Kebbi da jihar Sokoto dake makwabta.

Yan kungiyar na kai hare-hare daga sansanin su a cikin daji tare da satar dabbobi da kuma tilastawa mazauna biyan haraji.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp