Home Labarai Hukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatanta

Hukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatanta

Hukumar Jin daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta bayyana ranar 13 ga Mayu, 2026 a matsayin ranar da za a fara jigilar rukunin farko na alhazan jihar zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.

Babban daraktan hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyara ta aiki da ya kai majalisar dokokin Jihar Kano, bisa ga jadawalin jigilar alhazai da hukumar Alhazai ta Ƙasa ta fitar kamar yadda mai magana da yawun hukumar a Kano Sulaiman A Dederi ya sanar.

Ya bayyana cewa hukumar ta kammala dukkan muhimman shirye-shirye da suka haɗa da tantance takardu,da tsare-tsaren jigila, da wayar da kai, da gwajin lafiya da kuma sauran matakan da suka dace domin tabbatar da an gudanar da aikin cikin tsari da kwanciyar hankali.

Alhaji Matawalle ya jaddada cewa yin bayani ga majalisar dokoki musamman Kwamitin Hajji kafin fara jigilar alhazai al’ada ce mai karfafa guiwa da kuma tabbatar da cewa dukkan shirye-shirye suna tafiya yadda aka tsara.

Ya kuma tabbatar da cewa zai yi amfani da gogewarsa a harkokin Hajji tare da bullo da sabbin tsare-tsare domin tabbatar da cewa alhazan Kano sun gudanar da ibadarsu cikin sauƙi, tsaro da cikakken kulawa.

Da yake jawabi tun da farko, Mataimakin Kakakin majalisar dokokin Jihar Kano kuma mamba a Kwamitin Hajji, Hon. Muhammad Bello Butu-Butu, ya taya babban daraktan murnar nadin da aka yi masa, yana mai bayyana cewa nadin ya dace da ƙwarewarsa da jajircewarsa.

Ya kuma tabbatar da cewa Majalisar za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da Hukumar domin ganin an cimma burin gudanar da Hajji cikin nasara da kwanciyar hankali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp