Home Labarai Hukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatanta

Hukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatanta

Hukumar Jin daɗin Alhazai ta Jihar Kano ta bayyana ranar 13 ga Mayu, 2026 a matsayin ranar da za a fara jigilar rukunin farko na alhazan jihar zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2026.

Babban daraktan hukumar, Alhaji Abubakar Ibrahim Matawalle, ne ya bayyana hakan yayin wata ziyara ta aiki da ya kai majalisar dokokin Jihar Kano, bisa ga jadawalin jigilar alhazai da hukumar Alhazai ta Ƙasa ta fitar kamar yadda mai magana da yawun hukumar a Kano Sulaiman A Dederi ya sanar.

Ya bayyana cewa hukumar ta kammala dukkan muhimman shirye-shirye da suka haɗa da tantance takardu,da tsare-tsaren jigila, da wayar da kai, da gwajin lafiya da kuma sauran matakan da suka dace domin tabbatar da an gudanar da aikin cikin tsari da kwanciyar hankali.

Alhaji Matawalle ya jaddada cewa yin bayani ga majalisar dokoki musamman Kwamitin Hajji kafin fara jigilar alhazai al’ada ce mai karfafa guiwa da kuma tabbatar da cewa dukkan shirye-shirye suna tafiya yadda aka tsara.

Ya kuma tabbatar da cewa zai yi amfani da gogewarsa a harkokin Hajji tare da bullo da sabbin tsare-tsare domin tabbatar da cewa alhazan Kano sun gudanar da ibadarsu cikin sauƙi, tsaro da cikakken kulawa.

Da yake jawabi tun da farko, Mataimakin Kakakin majalisar dokokin Jihar Kano kuma mamba a Kwamitin Hajji, Hon. Muhammad Bello Butu-Butu, ya taya babban daraktan murnar nadin da aka yi masa, yana mai bayyana cewa nadin ya dace da ƙwarewarsa da jajircewarsa.

Ya kuma tabbatar da cewa Majalisar za ta ci gaba da aiki kafada da kafada da Hukumar domin ganin an cimma burin gudanar da Hajji cikin nasara da kwanciyar hankali.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp