Home Labarai Dangote ya ƙara farashin man fetur

Dangote ya ƙara farashin man fetur

Matatar man Dangote ta ƙara farashin man fetur daga naira 774 zuwa naira 874 kan kowanne lita, lamarin da ya haifar da damuwa game da yiwuwar tashin farashin fetur a faɗin Najeriya.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa wani babban jami’in matatar ya tabbatar da sabon farashin a ranar Litinin, inda ya ce an ɗauki matakin ne saboda rashin tabbas da hauhawar farashin man a kasuwannin duniya sakamakon rikicin Gabas ta Tsakiya.

Binciken petroleumprice.ng ya nuna cewa an riga an fara amfani da sabon farashin, wanda zai iya shafar dillalan sayarwa da kuma masu amfani da fetur a ƙasar baki ɗaya.

Ƙarin farashin ya biyo bayan dakatarwar da matatar ta yi kan lodin fetur daga karfe 12 na dare a ranar 2 ga Maris, 2026, sakamakon farashin mai a duniya da ya wuce dala 80 a kan kowanne ganga cikin dare ɗaya.

Masu sayar da fetur a kasuwannin unguwanni sun bayyana fargaba cewa wannan ƙaruwa na iya kawo ƙarancin mai a wasu wurare, musamman a lokutan da ake da yawan buƙata, inda wasu ke ganin cewa hakan na iya ƙara matsaloli ga masu amfani da motoci da kamfanonin sufuri a Najeriya.

Haka zalika, masana tattalin arziki sun yi gargadi cewa ƙarin farashin zai iya janyo hauhawar wasu kayan more rayuwa, wanda zai ƙara tsananta halin tattalin arziki ga talakawa da ‘yan kasuwa a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp