Home Labarai Dangote ya ƙara farashin man fetur

Dangote ya ƙara farashin man fetur

Matatar man Dangote ta ƙara farashin man fetur daga naira 774 zuwa naira 874 kan kowanne lita, lamarin da ya haifar da damuwa game da yiwuwar tashin farashin fetur a faɗin Najeriya.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa wani babban jami’in matatar ya tabbatar da sabon farashin a ranar Litinin, inda ya ce an ɗauki matakin ne saboda rashin tabbas da hauhawar farashin man a kasuwannin duniya sakamakon rikicin Gabas ta Tsakiya.

Binciken petroleumprice.ng ya nuna cewa an riga an fara amfani da sabon farashin, wanda zai iya shafar dillalan sayarwa da kuma masu amfani da fetur a ƙasar baki ɗaya.

Ƙarin farashin ya biyo bayan dakatarwar da matatar ta yi kan lodin fetur daga karfe 12 na dare a ranar 2 ga Maris, 2026, sakamakon farashin mai a duniya da ya wuce dala 80 a kan kowanne ganga cikin dare ɗaya.

Masu sayar da fetur a kasuwannin unguwanni sun bayyana fargaba cewa wannan ƙaruwa na iya kawo ƙarancin mai a wasu wurare, musamman a lokutan da ake da yawan buƙata, inda wasu ke ganin cewa hakan na iya ƙara matsaloli ga masu amfani da motoci da kamfanonin sufuri a Najeriya.

Haka zalika, masana tattalin arziki sun yi gargadi cewa ƙarin farashin zai iya janyo hauhawar wasu kayan more rayuwa, wanda zai ƙara tsananta halin tattalin arziki ga talakawa da ‘yan kasuwa a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp