Home Labarai Dangote ya ƙara farashin man fetur

Dangote ya ƙara farashin man fetur

Matatar man Dangote ta ƙara farashin man fetur daga naira 774 zuwa naira 874 kan kowanne lita, lamarin da ya haifar da damuwa game da yiwuwar tashin farashin fetur a faɗin Najeriya.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa wani babban jami’in matatar ya tabbatar da sabon farashin a ranar Litinin, inda ya ce an ɗauki matakin ne saboda rashin tabbas da hauhawar farashin man a kasuwannin duniya sakamakon rikicin Gabas ta Tsakiya.

Binciken petroleumprice.ng ya nuna cewa an riga an fara amfani da sabon farashin, wanda zai iya shafar dillalan sayarwa da kuma masu amfani da fetur a ƙasar baki ɗaya.

Ƙarin farashin ya biyo bayan dakatarwar da matatar ta yi kan lodin fetur daga karfe 12 na dare a ranar 2 ga Maris, 2026, sakamakon farashin mai a duniya da ya wuce dala 80 a kan kowanne ganga cikin dare ɗaya.

Masu sayar da fetur a kasuwannin unguwanni sun bayyana fargaba cewa wannan ƙaruwa na iya kawo ƙarancin mai a wasu wurare, musamman a lokutan da ake da yawan buƙata, inda wasu ke ganin cewa hakan na iya ƙara matsaloli ga masu amfani da motoci da kamfanonin sufuri a Najeriya.

Haka zalika, masana tattalin arziki sun yi gargadi cewa ƙarin farashin zai iya janyo hauhawar wasu kayan more rayuwa, wanda zai ƙara tsananta halin tattalin arziki ga talakawa da ‘yan kasuwa a ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp