Home General Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara...

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Hukumar kare haƙƙin ɗan adam ta Najeriya NHRC ta sanar da karɓar ƙorafe-ƙorafen take haƙƙin ɗan adama har dubu 3 da 19 tsakanin watan Janairu zuwa Disamban shekarar da ta gabata a jihar Kano kaɗai.

Cikin ƙorafe-ƙorafen da ke gaban hukumar masu alaƙa da cin zarafin mata da ƙananan yara su ne kan gaba a jihar ta Kano, kamar yadda alƙaluman hukumar ke nunawa.

Shugaban hukumar a jihar ta Kano Shehu Abdullahi da ke sanar da hakan ga manema labarai a yau Litinin ya ce cikin ƙorafe-ƙorafen fiye da dubu 3 da aka gabatar gabansu sun yi nasarar magance dubu 2 da 276.

Shugaban hukumar ta NHRC a Kano, ya kuma ce yanzu haka hukumar na aiki kan ƙorafe-ƙorafe 743 da basu kai ga kammala warwarewa ba.

A cewar shugaban na NHRC galibin ƙorafe-ƙorafen da aka fiya miƙa musu a jihar ta Kano sun fi shafar batutuwa masu alaƙa da watsi da baiwa yara kulawa, ko kuma take haƙƙin yaran, kana cin zarafi a cikin gidajen aure sai take haƙƙin zamantakewa ko na rayuwa sai kuma batutuwa masu alaƙa da al’adu da zamantakewar iyali.

Shugaban na NHRC ya ce sauran ƙorafe-ƙorafen da hukumar ke samu sun shafi cin zarafi daga jami’an tsaro, cin zarafi ta hanyar lalata musamman ga mata kana matsalar iyaye ta rashin ɗaukar nauyin iyalansu da sauran ƙorafe-ƙorafe masu alaka da rayuwar yau da kullum.

Shugaban hukumar kare haƙƙin bil’adaman ta Najeriya rashen jihar Kano Abdullahi Shehu ya sha alwashin ɗaukar gaɓarar fara aikin wayar da kan jama’a hatta a yankunan karkara ciki har da shirya taruka na musamman don ankarar da jama’a kan haƙƙoƙinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp