Home General Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara...

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Hukumar kare haƙƙin ɗan adam ta Najeriya NHRC ta sanar da karɓar ƙorafe-ƙorafen take haƙƙin ɗan adama har dubu 3 da 19 tsakanin watan Janairu zuwa Disamban shekarar da ta gabata a jihar Kano kaɗai.

Cikin ƙorafe-ƙorafen da ke gaban hukumar masu alaƙa da cin zarafin mata da ƙananan yara su ne kan gaba a jihar ta Kano, kamar yadda alƙaluman hukumar ke nunawa.

Shugaban hukumar a jihar ta Kano Shehu Abdullahi da ke sanar da hakan ga manema labarai a yau Litinin ya ce cikin ƙorafe-ƙorafen fiye da dubu 3 da aka gabatar gabansu sun yi nasarar magance dubu 2 da 276.

Shugaban hukumar ta NHRC a Kano, ya kuma ce yanzu haka hukumar na aiki kan ƙorafe-ƙorafe 743 da basu kai ga kammala warwarewa ba.

A cewar shugaban na NHRC galibin ƙorafe-ƙorafen da aka fiya miƙa musu a jihar ta Kano sun fi shafar batutuwa masu alaƙa da watsi da baiwa yara kulawa, ko kuma take haƙƙin yaran, kana cin zarafi a cikin gidajen aure sai take haƙƙin zamantakewa ko na rayuwa sai kuma batutuwa masu alaƙa da al’adu da zamantakewar iyali.

Shugaban na NHRC ya ce sauran ƙorafe-ƙorafen da hukumar ke samu sun shafi cin zarafi daga jami’an tsaro, cin zarafi ta hanyar lalata musamman ga mata kana matsalar iyaye ta rashin ɗaukar nauyin iyalansu da sauran ƙorafe-ƙorafe masu alaka da rayuwar yau da kullum.

Shugaban hukumar kare haƙƙin bil’adaman ta Najeriya rashen jihar Kano Abdullahi Shehu ya sha alwashin ɗaukar gaɓarar fara aikin wayar da kan jama’a hatta a yankunan karkara ciki har da shirya taruka na musamman don ankarar da jama’a kan haƙƙoƙinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp