Home Labarai Ƴansanda a jihar Nasarawa sun tseratar da yara 17 da ake shirin...

Ƴansanda a jihar Nasarawa sun tseratar da yara 17 da ake shirin safararsu

Rundunar Ƴansandan jihar Nasarawa ta sami nasarar tserar da wasu mutane 17 da ake kan hanyar safararsu daga jihar yayin wani binciken ababen hawa da suka gudanar a ƙaramar hukumar Karu ta jihar.

Wannan na cikin wata sanarwar da rundunar ƴansandan ta fitar, wadda ta ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar ɗin da ta gabata da misalin ƙarfe 5 da mintuna 50 lokacin da jami’anta ke tsaka da binciken ababen hawa a dai dai Mararaba inda suka ci karo da motar ƙirar Volkswagen Sharon mai lamba SHD 253 YU maƙare da mutanen su 17.

Sanarwar ta ci gaba da cewa bayan dogayen tambayoyi ne suka gano cewa babu gaskiya a tare da matuƙin motar wanda aka bayyana sunanshi da Nanle John mai shekaru 36, da ke ɗauke da fasinjan su 17 galibinsu ƙananan yara da suka ƙunshi Maza 11 da Mata 6 da ke a tsakanin shekarun 10 zuwa 19.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin kakakin rundunar ƴansandan jihar ta Nasarawa Ramhan Nansel tun farko sun yi zargin babu gaskiya a cikin yanayin bulaguron fasinjan da ke cikin motar hakan ya sanya su tsananta bincike inda suka gano cewa safarar yaran ake shirin yi.

Daga bayanan da aka samu daga mutanen, sun shaidawa rundunar ƴansandan cewa an ɗebo su ne daga yankin Shendam na jihar Pulato kuma suna kan hanyar zuwa Kayama ne a jihar Kwara inda za a damƙa su a hannun wasu mutum mai suna Umaru da ya yi alƙawarin samar musu aikin noma a ƙauyensu.

Duk ƙoƙarin da rundunar ƴansandan ta yi wajen tuntuɓar iyayen yaran da ke cikin motar yaci tura lura da yadda aka gaza samunsu a lambobin wayar da aka baiwa jami’an.

Mr Nansel ya ce tuni suka tsare ilahirin yaran su 17 yayinda Kwamishinan ƴansanda na jihar Shetima Mohammed ya umarci tsananta bincike don gano masu hannu a safarar tare da sada yaran da iyayensu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp