Home Labarai Ƴansanda a jihar Nasarawa sun tseratar da yara 17 da ake shirin...

Ƴansanda a jihar Nasarawa sun tseratar da yara 17 da ake shirin safararsu

Rundunar Ƴansandan jihar Nasarawa ta sami nasarar tserar da wasu mutane 17 da ake kan hanyar safararsu daga jihar yayin wani binciken ababen hawa da suka gudanar a ƙaramar hukumar Karu ta jihar.

Wannan na cikin wata sanarwar da rundunar ƴansandan ta fitar, wadda ta ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar ɗin da ta gabata da misalin ƙarfe 5 da mintuna 50 lokacin da jami’anta ke tsaka da binciken ababen hawa a dai dai Mararaba inda suka ci karo da motar ƙirar Volkswagen Sharon mai lamba SHD 253 YU maƙare da mutanen su 17.

Sanarwar ta ci gaba da cewa bayan dogayen tambayoyi ne suka gano cewa babu gaskiya a tare da matuƙin motar wanda aka bayyana sunanshi da Nanle John mai shekaru 36, da ke ɗauke da fasinjan su 17 galibinsu ƙananan yara da suka ƙunshi Maza 11 da Mata 6 da ke a tsakanin shekarun 10 zuwa 19.

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin kakakin rundunar ƴansandan jihar ta Nasarawa Ramhan Nansel tun farko sun yi zargin babu gaskiya a cikin yanayin bulaguron fasinjan da ke cikin motar hakan ya sanya su tsananta bincike inda suka gano cewa safarar yaran ake shirin yi.

Daga bayanan da aka samu daga mutanen, sun shaidawa rundunar ƴansandan cewa an ɗebo su ne daga yankin Shendam na jihar Pulato kuma suna kan hanyar zuwa Kayama ne a jihar Kwara inda za a damƙa su a hannun wasu mutum mai suna Umaru da ya yi alƙawarin samar musu aikin noma a ƙauyensu.

Duk ƙoƙarin da rundunar ƴansandan ta yi wajen tuntuɓar iyayen yaran da ke cikin motar yaci tura lura da yadda aka gaza samunsu a lambobin wayar da aka baiwa jami’an.

Mr Nansel ya ce tuni suka tsare ilahirin yaran su 17 yayinda Kwamishinan ƴansanda na jihar Shetima Mohammed ya umarci tsananta bincike don gano masu hannu a safarar tare da sada yaran da iyayensu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp