Home Labarai Sojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

Sojoji sun lalata sansanonin ƴanbindiga a Arewa maso Gabashin Najeriya

Rundunar sojin Najeriya ta ce sojojin haɗin gwiwarta ta Operation haɗin kai da JTF a Arewa maso Gabashin ƙasar sun samu nasarori a gagarumin samamen da suka gudanar da ake kira da Operation DESERT SANITY, inda suka lalata sansanonin ‘yanbindiga da dama tare da ƙwace makamai da kayan yaƙi.

Sojojin sun kuma daƙile hare-haren da aka shirya a yankin Timbuktu Triangle a lokacin samamen.

Sanarwar da rundunar ta fitar wa manema labarai ta ce a ranar Lahadi, 18 ga Janairu, 2026, sojoji sun tashi daga wuraren da suke tsarewa inda suka gudanar da samamen bisa bayanan sirri a kan wasu sansanonin ‘yanbindiga da aka gano, ciki har da Chilaria, Garin Faruk da Abirma.

A yayin samamen, an samu kwatar kayan soji da dama, ciki har da wayoyi, rediyo, harsasai, bindigogi na AK-47 guda 5, tutocin Boko Haram/ISWAP, kayan aikin noma, motar daukar kaya, da man fetur, da sauran kayayyakin yaƙi na ‘yanbindiga.

Sojojin sun fuskanci harin jiragen sama marasa matuki daga ‘yanbindiga a lokacin samamen, amma hakan bai hana su ci gaba da gudanar da ayyukansu ba.

Haka kuma, an dakile wani harin a yammacin ranar, wanda ya tilasta wa ‘yanbindiga ja da baya, abin da ya nuna cikakken rinjayar sojoji a yankin da kuma ƙarfin su wajen tabbatar da tsaro da zaman lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp