Home Labarai Tinubu ya yi tir da kisan mace da ƴaƴanta shida a Kano

Tinubu ya yi tir da kisan mace da ƴaƴanta shida a Kano

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kakkausar suka kan kisan gilla da aka yi wa wata matar aure mai suna Fatima Abubakar, da ƴaƴanta shida a unguwar Chiranci da ke Jihar Kano.

Cikin wata sanarwa da fadarsa ta fitar, Shugaba Tinubu ya bayyana lamarin a matsayin mummunan rashin imani da rashin tausayi, wanda ya girgiza al’umma da ma ƙasa baki ɗaya kuma ya saɓa wa ƙa’idojin bil’adama.

Tinubu ya nuna matuƙar alhini kan wannan mummunan iftila’in, tare da miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.

Shugaban ya kuma yaba wa rundunar ƴansandan Najeriya bisa gaggawar ɗaukar matakin da ya kai ga kama manyan waɗanda ake zargi da aikata laifin.

Ya umarci hukumomin tsaro da su tabbatar da gudanar da cikakken bincike tare da gurfanar da duk wanda aka samu da hannu a cikin kisan a gaban kotu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp