Home Labarai Kisan gilla – Ƴansandan jihar Kano sun kama wadanda ake zargi da...

Kisan gilla – Ƴansandan jihar Kano sun kama wadanda ake zargi da ƴaƴanta

Rundunar ƴan sanda jihar Kano ta tabbatar da kama mutum uku da take zargi da aikata kisan gilla ga wata mata da ƴaƴanta 6 a unguwar dorayi Chiranci dake jihar.

Kakakin Rundunar CSP Abdullah Haruna kiyawa ne ya tabbata da hakan ta cikin wata sanarwar da ya fitar a safiyar Lahadi.

Sanarwar ta ce dakarun rundunar sun kama Umar Auwalu mai shekara 23 dan unguwar sabuwar Gandun dake Kano da Isyaku Yakubu wanda aka fi sani da Chebe dan unguwar Sagagi sai kuma Yakubu Abdul’aziz wanda ake kira da wawo Mai kimanin shekaru 21 dan unguwar sabon gida Sharada.

Wanda ake zargi da jagorantar wannan kisa wanda dan uwa ga Matar Auren da aka hallaka ya amsa laifinsa wanda yace su suka aikata kisan kan da aka yi ta hanyar kone Wasu matan aure biyu a unguwar tudun Yola dake jihar Kano.

Rundunar ta ce ta samu makamai da suka haɗar da hira, Adda da kuma kuma wasu kuɗi da suka yi fashinsu a lokacin, sai kuma muggan makamai da yanzu haka ake bincike akansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp