Home Labarai Ƴan sanda sun fara bincike kan mutum 6 da aka yiwa yankan...

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutum 6 da aka yiwa yankan rago a Jihar

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta ce ta fara bincike kan wani mummunan kisa da ya auku a unguwar Dorayi Chiranchi dake jihar Kano a ranar asabar.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu da ba a san ko su wane ba sun shiga gidan Haruna Bashir, inda suka kai hari kan Fatima Abubakar mai shekaru 35 da ’ya’yanta shida, lamarin da ya yi sanadin rasuwarsu.

Shaidun gani da ido sun bayyana cewa lamarin ya faru ne inda maharan suka shiga gidan ba tare da an gano su ba, suka aikata wannan ta’asa kafin su tsere daga wurin.
Maƙwabta sun ce sun farga ne da jin ihun mutane da kukan neman taimako, amma kafin a kai dauki, an riga an yi mummunan lahani.

Waɗanda abin ya rutsa da su sun haɗa da Fatima Kabir, matar gidan mai kimanin shekaru 35, sai babbar ‘yarta Maimuna Haruna da ƙanwarta. Aisha Haruna da ƙannenta maza Bashir da Abubakar, sai kuma jariri wanda ake goyo wanda aka jefa shi a rijiya bayan an kashe shi.

Jami’an tsaro sun isa wurin bayan samun rahoton faruwar lamarin, inda suka killace yankin domin fara bincike.

An kuma kwashe gawarwakin mamatan zuwa asibiti domin tantancewa da kuma shirya musu jana’iza kamar yadda addinin musulunci ya tanada.

Al’ummar yankin sun nuna matuƙar alhini da damuwa kan wannan lamari, inda da dama ke kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su ƙara tsaurara matakan tsaro, domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Hukumar ’yan sanda ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce ta fara bincike mai zurfi domin gano waɗanda suka aikata laifin.

Ta kuma yi kira ga jama’a da su bayar da duk wani bayani da zai taimaka wajen cafke masu hannu a wannan aika-aika.

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wanda aka kama, yayin da bincike ke ci gaba. Al’umma na ci gaba da nuna alhini da jimami, tare da addu’a ga mamatan da kuma fatan ganin adalci ya tabbata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp