Home Labarai Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara aikin sabuwar dokar haraji

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da tsare-tsare da za a yi amfani da su wajen aiwatar da sabbin dokokin haraji, tana mai kafa hujja da wasu rashin tabbas kan matakan ƙarshe da aka bijiro da su cikin sabuwar dokar.

Shugaban Kwamitin Shugaban Ƙasa kan tsarin harajin, Taiwo Oyedele ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai a birnin Legas, yana mai cewa akwai nazarce-nazarce da ya kamata a kammala bibiya kafin fara aiwatar da dokar.

Oyedele ya ce tuni ya shaida wa hukumomin da ke da ruwa da tsaki a ɓangaren haraji su dakata da duk wani aiki da ya shafi wannan doka.

Dokar haraji ta Najeriya, wadda ta fara aiki a ranar 1 ga Janairu, ta fuskanci suka bayan zargin cewa anyi sauye-sauye da majalisar dokokin ƙasar ta amince da su, akwai ɗungushe a ciki.

Sai dai Oyedele ya nuna damuwa kan yadda wannan mataki ke fuskantar caccaka, yana mai danganta hakan da yaɗa labaran ƙarya da nufin kawo cikas ga sabon tsarin harajin.

Ya ce yadda aka riƙa yamaɗiɗin labaran ƙarya a bara, hakan ya sanya Najeriya yin asarar Naira tiriliyan 4.6 a rana guda cikin watan Nuwamba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp