Home Labarai Kwankwaso ya zargi yadda ake matsawa wasu shuwagabannin kananan hukumomi a jihar...

Kwankwaso ya zargi yadda ake matsawa wasu shuwagabannin kananan hukumomi a jihar Kano

Tsohon Gwamnan Jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya zargi yadda yace ana matsa wa wasu shugabannin ƙananan hukumomi lamba domin su fice daga tsarin Kwankwasiyya.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a yau Talata, cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta.

In da ya ce ya samu kiraye-kiraye daga wasu shugabannin ƙananan hukumomi da kuma ’yan Majalisar Jiha, inda ake buƙatar su sanya hannu domin komawa jam’iyyar APC.

Ya ƙara da cewa yana ƙarfafa gwiwar masu ci gaba da kasancewa cikin tsarin Kwankwasiyya, tare da ba su tabbacin cewa za su yi aiki tare domin fuskantar zaɓen shekarar 2027 mai zuwa.

Daga bisani Kwankwaso ya yabawa Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya yabi Gwamnatinsa ya kuma kushe gwamnatin da ta gabata.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp