Home Labarai Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

‘Yan uwan wata mata Aishatu Umar, sun koka kan yadda suke zargin likitoci a asibitin Abubakar Imam sun manta Almakashi a Cikin ‘yar’uwarsu, abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Ta cikin wani rubutu a shafin facebook da Abubakar Muhammad, ɗan’uwa ga marigayiyar ya wallafa, ya zargi sakacin likitocin matsayin abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Yace a watan Satumbar daya gabata ne, aka yiwa Aisha aikin tiyata a Asibitin ƙwararun na Abubakar Imam dake Kano, al’amarin da daga baya ha dinga haifar mata da matsanancin ciwon mara.

Bayan ƙorafe-ƙorafe da yace mariganyar ta yi ga likitocin asibitin lokuta da dama amman suna nuna ba wata matsala, sai daga baya suka yanke shawarar zuwa a ɗau gwajin hoton cikin, inda anan ne aka gane almakashin fiɗa aka bari a cikinta bayan tiyatar. Gano hakan ya faru ne kwanaki biyu kafin rasuwarta.

Sai dai bayan fitar labarin, hukumar dake lura da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da bincike akan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp