Home Labarai Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

‘Yan uwan wata mata Aishatu Umar, sun koka kan yadda suke zargin likitoci a asibitin Abubakar Imam sun manta Almakashi a Cikin ‘yar’uwarsu, abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Ta cikin wani rubutu a shafin facebook da Abubakar Muhammad, ɗan’uwa ga marigayiyar ya wallafa, ya zargi sakacin likitocin matsayin abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Yace a watan Satumbar daya gabata ne, aka yiwa Aisha aikin tiyata a Asibitin ƙwararun na Abubakar Imam dake Kano, al’amarin da daga baya ha dinga haifar mata da matsanancin ciwon mara.

Bayan ƙorafe-ƙorafe da yace mariganyar ta yi ga likitocin asibitin lokuta da dama amman suna nuna ba wata matsala, sai daga baya suka yanke shawarar zuwa a ɗau gwajin hoton cikin, inda anan ne aka gane almakashin fiɗa aka bari a cikinta bayan tiyatar. Gano hakan ya faru ne kwanaki biyu kafin rasuwarta.

Sai dai bayan fitar labarin, hukumar dake lura da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da bincike akan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp