Home Labarai Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

Likitoci sun manta almakashi a cikin wata mata a Kano

‘Yan uwan wata mata Aishatu Umar, sun koka kan yadda suke zargin likitoci a asibitin Abubakar Imam sun manta Almakashi a Cikin ‘yar’uwarsu, abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Ta cikin wani rubutu a shafin facebook da Abubakar Muhammad, ɗan’uwa ga marigayiyar ya wallafa, ya zargi sakacin likitocin matsayin abin da yayi sanadiyyar mutuwarta.

Yace a watan Satumbar daya gabata ne, aka yiwa Aisha aikin tiyata a Asibitin ƙwararun na Abubakar Imam dake Kano, al’amarin da daga baya ha dinga haifar mata da matsanancin ciwon mara.

Bayan ƙorafe-ƙorafe da yace mariganyar ta yi ga likitocin asibitin lokuta da dama amman suna nuna ba wata matsala, sai daga baya suka yanke shawarar zuwa a ɗau gwajin hoton cikin, inda anan ne aka gane almakashin fiɗa aka bari a cikinta bayan tiyatar. Gano hakan ya faru ne kwanaki biyu kafin rasuwarta.

Sai dai bayan fitar labarin, hukumar dake lura da asibitocin jihar Kano ta bayar da umarnin gudanar da bincike akan lamarin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp